Home Taska Hukumar NITDA Ta Horar Da `Yan Jarida 50 Ilimin Gano Sahihancin Labarai...

Hukumar NITDA Ta Horar Da `Yan Jarida 50 Ilimin Gano Sahihancin Labarai A Jihar Jigawa

Hukumar NITDA Ta Horar Da `Yan Jarida 50 Ilimin Gano Sahihancin Labarai A Jihar Jigawa

A kokarin da ta ke yi wajen ci gaba da bunkasa kwarewar `yan jaridu akan harkar aikin jarida a zamanance, hukumar bunkasa fasahar sadarwar zamani ta kasa (NITDA), karkashin jagorancin Malam Kashif Inuwa Abdullahi, ta bai wa `yan jarida da matasa masu ilimi a sabbin kafafen sadarwa na zamani kimanin su 50 horo akan ilimin gano tushe, da sahihancin labarai a kafafen sadarwa na zamani.

Mahangar Arewa ta ruwaito cewar horon na tsawon yini biyu, wanda hukumar NITDA ta dauki nauyi, yayin da kamfanin sadarwa na “Image Marchant Promotions Limited” (IMPR) masu wallafa Mujallar (PRNigeria), da (Economic Confidential Magazine), sai kuma kamfanin (Penlight Centre for New Media Innovation) suka gabatar da bada horon.

An kuma gudanar da horon a dakin taro na cibiyar horar da ma’aikata ta Jihar Jigawa, inda aka koyawa masu tasiri na sabbin kafafen sadarwa na zamani, da `yan jaridu ilimi da dabarun gano tushen labari da sahihancinsa da kuma dabi’u da halaye na kwarai wajen amfani da kafafen sadarwa gami da salon tafikar da aikin jarida a zamani.

A jawabin da ta gabatar na bude taron bada horon, shugabar sashen hulda da al’umma ta hukumar (NITDA), Hajiya Hadiza Umar, ta bayyana cewa horon bunkasa kwarewa na daya daga cikin ayyuka da burukan hukumar.

Sauran wadanda su ka gabatar da jawabai sun hada da tsohon shugaban gidan Rediyon Jihar Jigawa, Alhaji Sabo Abdullahi Guri, inda ya hori `yan jaridu a Najeriya wajen dabbaka kwarewa da dabi’u na kwarai a fagen tafikar da ayyukan.

A nasa jawabin babban Editan kafar sadarwa ta (PRNigeria), Malam Yusha’u Shu’aib, ya hori masu amfani da sabbin kafafen sadarwa na zamani da `yan jaridu da su kasance masu kula da takatsantsan wajen ayyukansu domin gujewa labaran karya da keta alfarma.

Mista Samuel Adeyemi, sakataren yada labarai na ma’aikatar sadarwa ta kasa, (NIPR), reshen Jihar Legas, ya gargadi `yan jaridu da masu amfani da sabbin kafafen sadarwar na zamani da su zama masu kula da kiyayewa da mutanen da ka iya yin amfani da su wajen yada munanan manufofi da akidoji.

Shugaban sashen ayyuka na cibiyar (Penlight), Malam Ɗahiru M. Lawal, ya baje bayanai akan yadda ake amfani da fasahohi da manhajoji na zamani wajen gano asali da tushen labarai da hotuna masu motsi da marasa motsi domin a gujewa yada labaran karya hadi da fatan sanar da al’umma sahihan labarai na zahirin gaskiya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp