Home Taska Hukumar NITDA Ta Horar Da `Yan Jarida 50 Ilimin Gano Sahihancin Labarai...

Hukumar NITDA Ta Horar Da `Yan Jarida 50 Ilimin Gano Sahihancin Labarai A Jihar Jigawa

Hukumar NITDA Ta Horar Da `Yan Jarida 50 Ilimin Gano Sahihancin Labarai A Jihar Jigawa

A kokarin da ta ke yi wajen ci gaba da bunkasa kwarewar `yan jaridu akan harkar aikin jarida a zamanance, hukumar bunkasa fasahar sadarwar zamani ta kasa (NITDA), karkashin jagorancin Malam Kashif Inuwa Abdullahi, ta bai wa `yan jarida da matasa masu ilimi a sabbin kafafen sadarwa na zamani kimanin su 50 horo akan ilimin gano tushe, da sahihancin labarai a kafafen sadarwa na zamani.

Mahangar Arewa ta ruwaito cewar horon na tsawon yini biyu, wanda hukumar NITDA ta dauki nauyi, yayin da kamfanin sadarwa na “Image Marchant Promotions Limited” (IMPR) masu wallafa Mujallar (PRNigeria), da (Economic Confidential Magazine), sai kuma kamfanin (Penlight Centre for New Media Innovation) suka gabatar da bada horon.

An kuma gudanar da horon a dakin taro na cibiyar horar da ma’aikata ta Jihar Jigawa, inda aka koyawa masu tasiri na sabbin kafafen sadarwa na zamani, da `yan jaridu ilimi da dabarun gano tushen labari da sahihancinsa da kuma dabi’u da halaye na kwarai wajen amfani da kafafen sadarwa gami da salon tafikar da aikin jarida a zamani.

A jawabin da ta gabatar na bude taron bada horon, shugabar sashen hulda da al’umma ta hukumar (NITDA), Hajiya Hadiza Umar, ta bayyana cewa horon bunkasa kwarewa na daya daga cikin ayyuka da burukan hukumar.

Sauran wadanda su ka gabatar da jawabai sun hada da tsohon shugaban gidan Rediyon Jihar Jigawa, Alhaji Sabo Abdullahi Guri, inda ya hori `yan jaridu a Najeriya wajen dabbaka kwarewa da dabi’u na kwarai a fagen tafikar da ayyukan.

A nasa jawabin babban Editan kafar sadarwa ta (PRNigeria), Malam Yusha’u Shu’aib, ya hori masu amfani da sabbin kafafen sadarwa na zamani da `yan jaridu da su kasance masu kula da takatsantsan wajen ayyukansu domin gujewa labaran karya da keta alfarma.

Mista Samuel Adeyemi, sakataren yada labarai na ma’aikatar sadarwa ta kasa, (NIPR), reshen Jihar Legas, ya gargadi `yan jaridu da masu amfani da sabbin kafafen sadarwar na zamani da su zama masu kula da kiyayewa da mutanen da ka iya yin amfani da su wajen yada munanan manufofi da akidoji.

Shugaban sashen ayyuka na cibiyar (Penlight), Malam Ɗahiru M. Lawal, ya baje bayanai akan yadda ake amfani da fasahohi da manhajoji na zamani wajen gano asali da tushen labarai da hotuna masu motsi da marasa motsi domin a gujewa yada labaran karya hadi da fatan sanar da al’umma sahihan labarai na zahirin gaskiya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp