Home Taska Faɗawa Cikin Rijiya: Mutane 13 Sun Rasa Rayukansu Ana Tsaka da Shagalin...

Faɗawa Cikin Rijiya: Mutane 13 Sun Rasa Rayukansu Ana Tsaka da Shagalin Biki a Indiya

Captured Boko Haram spies by troops
Captured Boko Haram spies by troops

Faɗawa Cikin Rijiya: Mutane 13 Sun Rasa Rayukansu Ana Tsaka da Shagalin Biki a Indiya

Akalla mutum 13 ne suka rasa rayukansu bayan sun fada cikin wata rijiya yayin wani biki da ake yi a jihar Utter Pradesh da ke yammacin Indiya.

Yan sanda sun ce wadanda abin ya ritsa da su – duka mata ne da yara – na zaune kan murfin da aka rufe rijiyar da shi a lokacin da ya rufta saboda nauyin mutanen da ke kansa.

Lamarin ya faru ne ranar Laraba da yamma a lokacin bikin gargajiya na “haldi”, inda ‘yan uwa suke shafa wa ango da amarya ruwan kurkur a fuska a matsayin alamar samun wadata.

Wasu karin mutum biyu sun jikkata a hatsarin, wanda ya faru a gundumar Kushinagar.

Firaminista Narendra Modi ya bayyana mutuwar tasu a matsayin “mai sosa zuciya”.

Lokacin da murfin ya karye, sauran baki sun ruga don ceto mutanen, inda suka kai su wani asibiti da ke kusa. Yayin da aka sanar da mutuwar mutum 11 nan take, wasu biyu kuma sun mutu a asibit, in ji ‘yan sanda.

Babban Ministan Utter Pradesh Yogi Adityanath ya nemi shugabannin ananan hukumomi da su taimaka wa iyalan mutanen da abin ya ritsa da su.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp