Home SIYASA Ɓangaren Gwamna Ganduje ya yi nasara a kotun ɗaukaka ƙara Kan Rikicin...

Ɓangaren Gwamna Ganduje ya yi nasara a kotun ɗaukaka ƙara Kan Rikicin APC a Kano

Ɓangaren Gwamna Ganduje ya yi nasara a kotun ɗaukaka ƙara Kan Rikicin APC a Kano

Ɓangaren Gwamna Abudllahi Umar Ganduje ya yi nasara a ƙarar da ya shigar yana ƙalubalantar nasarar da wata kotun ta bai wa ɓangaren tshohon Gwamna Ibrahim Shekarau a rikicin jam’iyyar APC mai mulkin Jahar Kano.

A zaman da ta yi yau Alhamis a Abuja, Kotun Ɗaukaka Ƙara ta ce hukuncin da Babbar Kotun Abuja ta yi ba daidai ba ne sannan ta tabbatar da cewa shugabannin da ɓangaren Ganduje ya zaɓa su ne halastattu.

Hukuncin kotun na yau ya bai wa ɓangaren Ganduje nasara a duka ɓangarori ukun da suka ɗaukaka ƙarar a kan su, kamar yadda Barista Abdullahi Adamu Fagge ya shaida BBC Hausa – ɗaya daga cikin lauyoyin ɓangaren gwamna.

Tun da farko ɓangaren da Shekarau ke jagoranta ya shigar da uwar jam’iyyar ƙara da kwamatin shugbancinta na ƙasa da kuma sakatarenta a ɓangare ɗaya, sannan suka shigar da shugabancin APC na Kano a ɗaya ɓangaren, da kuma kwamatin da ya shirya zaɓen shugabancin jam’iyyar a Kano a wani ɓangaren daban.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp