Home Labarai Mutane 8 ‘Yan Bindiga Suka Kashe a Kasuwar Shanu – Gwamnatin Abia

Mutane 8 ‘Yan Bindiga Suka Kashe a Kasuwar Shanu – Gwamnatin Abia

Mutane 8 ‘Yan Bindiga Suka Kashe a Kasuwar Shanu – Gwamnatin Abia

Mutum aƙalla takwas ne ‘yan bindiga suka kashe a kasuwar shanu ta Jihar Abiya da ke kudu maso kudancin Najeriya ranar Talata, kamar yadda gwamnatin jihar ta tabbatar.

Jaridar Punch ta ruwaito Kwamashinan Yaɗa Labarai da Tsare-Tsare Eze Chikamnayo yana cewa an kai harin ne da misalin ƙarfe 11:35 na dare.

sai dai wasu mazauna yankin da BBC Hausa ta tattauna da su sun ce mutum 11 ne suka mutu a harin.

“A ranar Talata 15 ga watan Fabarairu da misalin ƙarfe 11:35 na dare, wasu ‘ya bindiga da ba a san ko su wane ne ba suka afka wa ‘yan kasuwa a Sabuwar Kasuwar Shanu ta Omumauzor da ke Ƙaramar Hukumar Ukwa ta Gabas,” in ji shi cikin wata sanarwa.

An kai harin ne kwana ɗaya kafin komawar jagoran ƙungiyar ‘yan tawaye ta Indigenous People of Biafra (IPOB), Nnamdi Kanu, gaban kotu don fuskantar tuhuma game da zargin ta’addanci a Abuja babban birnin ƙasar.

Hukumomi a ƙasar na zargin ɓangaren ‘yan bindiga na IPOB mai suna Eastern Security Network (ESN) da kai ire-iren waɗannan hare-hare.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp