Home Labarai Mutane 8 ‘Yan Bindiga Suka Kashe a Kasuwar Shanu – Gwamnatin Abia

Mutane 8 ‘Yan Bindiga Suka Kashe a Kasuwar Shanu – Gwamnatin Abia

Mutane 8 ‘Yan Bindiga Suka Kashe a Kasuwar Shanu – Gwamnatin Abia

Mutum aƙalla takwas ne ‘yan bindiga suka kashe a kasuwar shanu ta Jihar Abiya da ke kudu maso kudancin Najeriya ranar Talata, kamar yadda gwamnatin jihar ta tabbatar.

Jaridar Punch ta ruwaito Kwamashinan Yaɗa Labarai da Tsare-Tsare Eze Chikamnayo yana cewa an kai harin ne da misalin ƙarfe 11:35 na dare.

sai dai wasu mazauna yankin da BBC Hausa ta tattauna da su sun ce mutum 11 ne suka mutu a harin.

“A ranar Talata 15 ga watan Fabarairu da misalin ƙarfe 11:35 na dare, wasu ‘ya bindiga da ba a san ko su wane ne ba suka afka wa ‘yan kasuwa a Sabuwar Kasuwar Shanu ta Omumauzor da ke Ƙaramar Hukumar Ukwa ta Gabas,” in ji shi cikin wata sanarwa.

An kai harin ne kwana ɗaya kafin komawar jagoran ƙungiyar ‘yan tawaye ta Indigenous People of Biafra (IPOB), Nnamdi Kanu, gaban kotu don fuskantar tuhuma game da zargin ta’addanci a Abuja babban birnin ƙasar.

Hukumomi a ƙasar na zargin ɓangaren ‘yan bindiga na IPOB mai suna Eastern Security Network (ESN) da kai ire-iren waɗannan hare-hare.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp