Home Taska Abubuwa 5 da Kuke Bukata Kafin Shiga Aikin Soja a Najeriya

Abubuwa 5 da Kuke Bukata Kafin Shiga Aikin Soja a Najeriya

Abubuwa 5 da Kuke Bukata Kafin Shiga Aikin Soja a Najeriya

 

Rundunar sojojin Najeriya ta fitar da sanarwar daukar sabbin ma’aikata na shekarar 2022/2023.

An nemi wadanda ke da sha’awar shiga aikin soja su ziyarci shafin rundunar na yanar gizo don cike fom.

A nan, mun tattaro wasu abubuwa biyar da dole sai me neman aikin ya cike su

A ranar Talata, 8 ga watan Maris ne, rundunar sojojin Najeriya ta sanar da cewar shirinta na daukar ma’aikata na 2022/2023 na gudana a yanzu haka.

An bukaci wadanda ke sha’awar aikin da su ziyarci shafin daukar aiki na rundunar sojin domin ganin yadda za su nemi aikin, Daily trust ta rahoto.

Idan kana son shiga aiki soja, dole ka cike wadannan abubuwan bukata:

1. Dole ka kasance dan Najeriya sannan ka mallaki katin shaida na dan kasa.

2. Dole ka mallaki akalla kredit 5, ciki harda Ingilishi a jarrabawar WASSCE, GCE, NECO ko NAPTIB a zama da bai wuci biyu ba.

3. Dole mutum ya kasance da lafiyar jiki da na kwakwalwa kuma kada mutum ya yi kasa da mita 1.68 ga maza ko kuma 1.62 ga mata.

4. Dole mutum ya kasance tsakanin shekara 18 da 26.

5. Dole ne a cire fom din da aka cike ta yanar gizo, a sanya hannu akai sannan a zo dashi cibiyar jarrabawa yayin da aka fara tantance wadanda za su shiga aikin

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

Comments are closed.

Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp