Home Taska ‘Yan Sintiri Sun yi Ram da Masu Garkuwa 10 a Dajin Kwara

‘Yan Sintiri Sun yi Ram da Masu Garkuwa 10 a Dajin Kwara

‘Yan Sintiri Sun yi Ram da Masu Garkuwa 10 a Dajin Kwara

‘Yan sintiri a jihar Kwara sun yi ram da wasu mutum goma wadanda ake zarginsu da addabar yankunan Obbo-Aiyegunle zuwa Ekiti.

Kamar yadda kwamandan hukumar sintiri, Alhaji Saka Ibrahim ya sanar, an kama su ne a daji yayin da jami’ai suka kai samame.

Ya sanar da cewa har yanzu mutanensu suna cikin daji kuma za su mika wadanda aka kama ga jami’an ‘yan sanda.

Kwara – Wasu mutum goma da ake zargin masu garkuwa da mutane ne da suka addabi yankin Obbo-Aiyegunle zuwa Ekiti a jihar Kwara sun shiga hannun hukuma.

An damke su ne bayan samamen da jami’ai suka kai wata maboyarsu da ke daji inda ake zargin suna adana wadanda suka sace, Daily Trust ta ruwaito hakan.

Yankin a cikin kwanakin nan ya shahara ta yadda masu garkuwa da mutane ke sace mutane kuma a kan samu gawawwakinsu bayan an biya kudin fansa.

Kwamandan hukumar sintiri ta jihar Kwara, Alhaji Saka Ibrahim, ya tabbatar da aukuwar lamarin ta wata tattaunawar waya da Daily Trust.

Kamar yadda yace:

“An damke wasu mutum bakwai a ranar Talata yayin da aka cafke wasu uku a ranar Laraba. Amma har yanzu jami’anmu na duba dajin. Za mu mika su hannun ‘yan sanda idan sun fito daga dajin.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp