Home Taska ‘Yan Sintiri Sun yi Ram da Masu Garkuwa 10 a Dajin Kwara

‘Yan Sintiri Sun yi Ram da Masu Garkuwa 10 a Dajin Kwara

‘Yan Sintiri Sun yi Ram da Masu Garkuwa 10 a Dajin Kwara

‘Yan sintiri a jihar Kwara sun yi ram da wasu mutum goma wadanda ake zarginsu da addabar yankunan Obbo-Aiyegunle zuwa Ekiti.

Kamar yadda kwamandan hukumar sintiri, Alhaji Saka Ibrahim ya sanar, an kama su ne a daji yayin da jami’ai suka kai samame.

Ya sanar da cewa har yanzu mutanensu suna cikin daji kuma za su mika wadanda aka kama ga jami’an ‘yan sanda.

Kwara – Wasu mutum goma da ake zargin masu garkuwa da mutane ne da suka addabi yankin Obbo-Aiyegunle zuwa Ekiti a jihar Kwara sun shiga hannun hukuma.

An damke su ne bayan samamen da jami’ai suka kai wata maboyarsu da ke daji inda ake zargin suna adana wadanda suka sace, Daily Trust ta ruwaito hakan.

Yankin a cikin kwanakin nan ya shahara ta yadda masu garkuwa da mutane ke sace mutane kuma a kan samu gawawwakinsu bayan an biya kudin fansa.

Kwamandan hukumar sintiri ta jihar Kwara, Alhaji Saka Ibrahim, ya tabbatar da aukuwar lamarin ta wata tattaunawar waya da Daily Trust.

Kamar yadda yace:

“An damke wasu mutum bakwai a ranar Talata yayin da aka cafke wasu uku a ranar Laraba. Amma har yanzu jami’anmu na duba dajin. Za mu mika su hannun ‘yan sanda idan sun fito daga dajin.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp