Home SIYASA Har Yanzu ba mu Samu Sahihin Kwafin Takardar Hukuncin Kotu na Tsige...

Har Yanzu ba mu Samu Sahihin Kwafin Takardar Hukuncin Kotu na Tsige Gwamnan Ebonyi ba – INEC

Har Yanzu ba mu Samu Sahihin Kwafin Takardar Hukuncin Kotu na Tsige Gwamnan Ebonyi ba – INEC

 

Hukumar zabe INEC tace har yanzun ba ta samu sahihin kwafin takardar hukuncin Kotu na tsige gwamna Umahi ba.

Kwamishinan INEC na kasa ya ce da zaran sun samu takardar daga Kotu, za su kira zama domin nazari kanta.

Babbar Kotun tarayya dake zamanta a Abuja ta kwace kujerar gwamna da kuma mataimakinsa na jihar Ebonyi kan sauya sheka.

Abuja – Hukumar zabe mai zaman kanta ta ƙasa INEC tace har yanzun ba ta samu kwafin takardar hukuncin da babbar Kotun tarayya dake Abuja ta yanke kan Gwamna Dave Umahi da mataimakinsa ba.

Festus Okoye, Kwamishinan hukumar na ƙasa kuma shugaban kwamitin tara bayanai, ne ya faɗi haka yayin zantawa da hukumar dillancin labarai ta ƙasa (NAN) a Abuja.

Premium Times ta rahoto Mista Okoye na cewa INEC zata zauna kan lamarin da zaran ta karbi takardar hukuncin da Kotu ta yanke.

Kwamishinan INEC ɗin ya ce:

“Har yanzun ba’a aiko mana da kwafin hukuncin da ake cewa Kotu ta yanke ba. INEC zata zauna ta yi nazari da zaran an miƙa mata takardar hukuncin Kotu ta gaske.”

Ko wane hukunci Kotu ta yanke?

A ranar Talata, babbar kotun tarayya dake zaune a Abuja karkashin jagorancin mai shari’a Inyang Ekwo, ta umarci gwamnan Ebonyi, David Umahi, ya fice da ofis ɗin gwamna kan sauya shekar da ya yi daga PDP zuwa APC.

A hukuncin da Alkalin Kotun ya yanke, ya kuma umarci Mista Igwe da ya daina nuna kansa a matsayin mataimakin gwamnan jihar Ebonyi.

Mai Shari’a Ekwo, ya bayyana cewa tun da sun fice daga PDP, jam’iyyar da mutane suka zabe su karkashinta, kama ta ya yi mutanen biyu su yi murabus daga kan mukamanssu.

Ya kuma ƙara da cewa saɓa wa doka ne ɗan takarar da aka zaɓe shi a wani muƙami karkashin jam’iyyar siyasa kuma ya koma wata jam’iyya ta daban.

Ya ce kuri’un da gwamna Umahi ya samu a zaben 9 ga watan Maris, 2019 na jam’iyyar PDP ne ba na APC ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp