Home Taska Kamfanonin Sufurin Jirgin Sama Sun Soke Sauka da Tashin Jiragen Saboda Tsadar...

Kamfanonin Sufurin Jirgin Sama Sun Soke Sauka da Tashin Jiragen Saboda Tsadar Man Fetur a Najeriya

Kamfanonin Sufurin Jirgin Sama Sun Soke Sauka da Tashin Jiragen Saboda Tsadar Man Fetur a Najeriya

 

Da alama babu sauki nan kusa kan batun tsadar man fetur a Najeriya, matsalar da ta tilasta wa kamfanonin sufurin jirgin sama kara farashin tikitinsu a kwanakin baya.

Kamfanonin sun ce a jiya sun yi mamaki bayan da aka sanar da su cewa an kara farashin man jirgin saman, inda ake sayar da shi kan naira 607 kan kowace lita a Kano a jiya.

Wannan ya kasance karin fiye da naira 100 cikin kwana guda.

Jaridar Daily Trust ta ce wasu masu kamfanoni sufurin jiragen saman sun sami sanarwar ce daga masu dillancin man a jiya, wadda ke sanar da su cewa farashin man na JetA1 ya karu zuwa naira 597 a Legas, kuma ya koma naira 599 a Abuja da Port Harcourt, sannan ya koma naira 607 a Kano.

A ranar Litinin an rika sayar da man kan naira 470 ne a Legas, inda a Kano kuwa naira 495 aka sayar da shi.

Wannan matakin ya janyo soke sauka da tashin jiragen sama a manya da kananan filayen jirgin sama na Najeriya.

Yawancin kamfanonin sufurin jirgin saman sun fitar da sanarwar da ke bayana halin da suka shiga kuma sun ba abokan huldarsu hakuri.

Kakakin kamfanin Azman Airline ya koka kan halin da suka sami kansu a ciki kuma ya ce babu yadda za su iya mayar da uwar kudin da suke zubawa balle ma su sami riba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp