Home Taska Kamfanonin Sufurin Jirgin Sama Sun Soke Sauka da Tashin Jiragen Saboda Tsadar...

Kamfanonin Sufurin Jirgin Sama Sun Soke Sauka da Tashin Jiragen Saboda Tsadar Man Fetur a Najeriya

Kamfanonin Sufurin Jirgin Sama Sun Soke Sauka da Tashin Jiragen Saboda Tsadar Man Fetur a Najeriya

 

Da alama babu sauki nan kusa kan batun tsadar man fetur a Najeriya, matsalar da ta tilasta wa kamfanonin sufurin jirgin sama kara farashin tikitinsu a kwanakin baya.

Kamfanonin sun ce a jiya sun yi mamaki bayan da aka sanar da su cewa an kara farashin man jirgin saman, inda ake sayar da shi kan naira 607 kan kowace lita a Kano a jiya.

Wannan ya kasance karin fiye da naira 100 cikin kwana guda.

Jaridar Daily Trust ta ce wasu masu kamfanoni sufurin jiragen saman sun sami sanarwar ce daga masu dillancin man a jiya, wadda ke sanar da su cewa farashin man na JetA1 ya karu zuwa naira 597 a Legas, kuma ya koma naira 599 a Abuja da Port Harcourt, sannan ya koma naira 607 a Kano.

A ranar Litinin an rika sayar da man kan naira 470 ne a Legas, inda a Kano kuwa naira 495 aka sayar da shi.

Wannan matakin ya janyo soke sauka da tashin jiragen sama a manya da kananan filayen jirgin sama na Najeriya.

Yawancin kamfanonin sufurin jirgin saman sun fitar da sanarwar da ke bayana halin da suka shiga kuma sun ba abokan huldarsu hakuri.

Kakakin kamfanin Azman Airline ya koka kan halin da suka sami kansu a ciki kuma ya ce babu yadda za su iya mayar da uwar kudin da suke zubawa balle ma su sami riba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp