Home Taska Kamfanonin Sufurin Jirgin Sama Sun Soke Sauka da Tashin Jiragen Saboda Tsadar...

Kamfanonin Sufurin Jirgin Sama Sun Soke Sauka da Tashin Jiragen Saboda Tsadar Man Fetur a Najeriya

Kamfanonin Sufurin Jirgin Sama Sun Soke Sauka da Tashin Jiragen Saboda Tsadar Man Fetur a Najeriya

 

Da alama babu sauki nan kusa kan batun tsadar man fetur a Najeriya, matsalar da ta tilasta wa kamfanonin sufurin jirgin sama kara farashin tikitinsu a kwanakin baya.

Kamfanonin sun ce a jiya sun yi mamaki bayan da aka sanar da su cewa an kara farashin man jirgin saman, inda ake sayar da shi kan naira 607 kan kowace lita a Kano a jiya.

Wannan ya kasance karin fiye da naira 100 cikin kwana guda.

Jaridar Daily Trust ta ce wasu masu kamfanoni sufurin jiragen saman sun sami sanarwar ce daga masu dillancin man a jiya, wadda ke sanar da su cewa farashin man na JetA1 ya karu zuwa naira 597 a Legas, kuma ya koma naira 599 a Abuja da Port Harcourt, sannan ya koma naira 607 a Kano.

A ranar Litinin an rika sayar da man kan naira 470 ne a Legas, inda a Kano kuwa naira 495 aka sayar da shi.

Wannan matakin ya janyo soke sauka da tashin jiragen sama a manya da kananan filayen jirgin sama na Najeriya.

Yawancin kamfanonin sufurin jirgin saman sun fitar da sanarwar da ke bayana halin da suka shiga kuma sun ba abokan huldarsu hakuri.

Kakakin kamfanin Azman Airline ya koka kan halin da suka sami kansu a ciki kuma ya ce babu yadda za su iya mayar da uwar kudin da suke zubawa balle ma su sami riba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp