Home SIYASA PDP ta Mika Sunayen Masu Maye Gurbin Gwamnan Jahar Ebonyi da Mataimakinsa

PDP ta Mika Sunayen Masu Maye Gurbin Gwamnan Jahar Ebonyi da Mataimakinsa

PDP ta Mika Sunayen Masu Maye Gurbin Gwamnan Jahar Ebonyi da Mataimakinsa

A yau ne kotu a Abuja ta ba da umarnin a tsige gwamnan jihar Ebonyi bayan da ya koma jam’iyyar APC daga PDP.

Tsigewar ta shafi mataimakinsa, wanda tare da mai gidan nasa suka koma APC; jam’iyya mai mulki a Najeriya.

Jam’iyyar PDP ta tura wa INEC sunayen wadanda take son su maye gurbin gwamna Umahi da mataimakinsa.

Jam’iyyar PDP ta ce ta mika sunayen mutanen da ta amince su maye gurbin gwamnan Ebonyi da mataimakinsa ga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), TheCable ta ruwaito.

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja, a ranar Talata, ta ba da umarnin tsige gwamnan Ebonyi, Dave Umahi, da mataimakinsa Eric Kelechi Igwe, biyo bayan sauya sheka da suka yi zuwa jam’iyyar APC.

Bayan faruwar lamarin, Shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Iyorchia Ayu, a wani taron manema labarai a ranar Talata, ya ce jam’iyyar ta zabi Iduma Igariwe da Fred Udogwu a madadin Umahi da Igwe domin ci gaba da mulkar jihar.

Wani bidiyon da PDP ta yada a shafinta na Twitter yana dauke da rubutu kamar haka:

“Bayan tsige Gwamna Dave Umahi da Mataimakinsa Mista Igwe na jihar Ebonyi, kuma bisa ga umarnin kotu, PDP ta mika wa INEC sunayen Iduma Igariwe da Fred Udogwu a matsayin sabon Gwamna da kuma mataimakin gwamnan Jihar Ebonyi”

Jam’iyyar APC a jihar Ebonyi, ta ce babu abin da zai kawo wani dan jam’iyyar PDP kusa da kujerar mulkin gwamnan jihar, kamar yadda Vanguard ta ruwaito.

Wannan na daya daga cikin lamurran da suke faruwa a APC tun bayan shillawar shugaban kasa Muhammadu Buhari birnin Landon domin duba lafiyarsa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp