Home Taska Gidauniyar Malam Inuwa ta Rabawa Marayu 100 Tallafin Turmin Atamfa 

Gidauniyar Malam Inuwa ta Rabawa Marayu 100 Tallafin Turmin Atamfa 

Tallafin Marayu

Gidauniyar Malam Inuwa ta Rabawa Marayu 100 Tallafin Turmin Atamfa 

 

A ƙoƙarin da ta ke kan cigaba da yi wajen ganin ta kyautatawa marayu a Jihar Jigawa a wannan wata na Ramadan mai albarka, Gidauniyar Malam Inuwa wacce mai girma shugaban hukumar bunƙasa fasahar sadarwar zamani ta ƙasa, (NITDA), Malam Kashif Inuwa Abdullahi, (CCIE) ya assasa, ta rabawa marayu mata (100) tallafin turmin Atamfa domin hidimar sallah a ƙaramar hukumar Haɗejia da ke Jihar Jigawa.

Rabon wanda aka gudanar a yammacin wannan rana, a ofishin gidauniyar da ke kan titin Garun-Gabas, Haɗejia, ya gudana ne a ƙarƙashin jagorancin shugabannin gidauniyar, da kwamitin marayu na ƙaramar hukumar waɗanda su ka zaƙulo marayun da su ka fi buƙatar temako a mazaɓun yankin gabaɗaya.

Marayun da su ka halarci wurin rabon su ka karɓa, da kuma wakilan marayun waɗanda su ka karɓa musu, gabaɗaya sun bayyana godiya da farin cikinsu tare da addu’ar fatan alkhairi ga mai girma shugaban hukumar ta (NITDA), Malam Kashif gami da fatan Allah Ya ji ƙan mahaifin nasa, Malam Inuwa Ya ƙara arziƙi.

Talata, 19 ga watan Afrelu, 2022.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp