Home Taska Gidauniyar Malam Inuwa ta Rabawa Marayu 100 Tallafin Turmin Atamfa 

Gidauniyar Malam Inuwa ta Rabawa Marayu 100 Tallafin Turmin Atamfa 

Tallafin Marayu

Gidauniyar Malam Inuwa ta Rabawa Marayu 100 Tallafin Turmin Atamfa 

 

A ƙoƙarin da ta ke kan cigaba da yi wajen ganin ta kyautatawa marayu a Jihar Jigawa a wannan wata na Ramadan mai albarka, Gidauniyar Malam Inuwa wacce mai girma shugaban hukumar bunƙasa fasahar sadarwar zamani ta ƙasa, (NITDA), Malam Kashif Inuwa Abdullahi, (CCIE) ya assasa, ta rabawa marayu mata (100) tallafin turmin Atamfa domin hidimar sallah a ƙaramar hukumar Haɗejia da ke Jihar Jigawa.

Rabon wanda aka gudanar a yammacin wannan rana, a ofishin gidauniyar da ke kan titin Garun-Gabas, Haɗejia, ya gudana ne a ƙarƙashin jagorancin shugabannin gidauniyar, da kwamitin marayu na ƙaramar hukumar waɗanda su ka zaƙulo marayun da su ka fi buƙatar temako a mazaɓun yankin gabaɗaya.

Marayun da su ka halarci wurin rabon su ka karɓa, da kuma wakilan marayun waɗanda su ka karɓa musu, gabaɗaya sun bayyana godiya da farin cikinsu tare da addu’ar fatan alkhairi ga mai girma shugaban hukumar ta (NITDA), Malam Kashif gami da fatan Allah Ya ji ƙan mahaifin nasa, Malam Inuwa Ya ƙara arziƙi.

Talata, 19 ga watan Afrelu, 2022.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp