Home Labarai Tsaro :Jirgin Sojin Sama ya Halaka Yara 6 a Jihar Niger

Tsaro :Jirgin Sojin Sama ya Halaka Yara 6 a Jihar Niger

Gwamnatin Jihar Niger ta tabbatar da mutuwar kananan yara 6 sakamakon wani hari da Rundunar Sojin Saman Nijeriya ta kai bisa kuskure.

Sakataren Gwamnatin Jihar, Ibrahim Matane ne ya bayyana mutuwar yaran, sakamakon harin jirgin saman. Inda yace lamarin ya auku ne makon daya gabata, inda bincike ya tabbatar da cewa yaran sun halaka ne sakamakon wani hari da dakarun sojin suka kai maboyar ‘yan Bindiga a jihar.

Lamarin dai ya faru ne a garin Kurebe dake karamar hukumar shiroro ta jihar Niger.

Ko da aka tambaye shi kan mutuwar yaran 6, cewa ko dai Dakarun Sojin Saman ne suka hallaka su: yace “ hakan zai iya kasancewa, don haka ne ma gwamnatin ke sake fadada bincike kan lamarin domin tabbatar da zahirin abinda ya faru.

A cewar shugaban kungiyar gamayyar kungiyoyin Karamar Hukumar ta Shiroro Salis Sambo, yayin da yake ganawa da manema labarai, yace Dakarun Sojin sun halaka yaran ne a kokarin da suke na tarwatsa ‘Yan Ta’adda wadanda suka gudu cikin al’umma domin tsira da rayuwar su.

Yace Kananan Yaran na kan hanyar su ta dawowa daga diban ruwa a wani gulmi, inda yace hudu cikin su ‘yan gida daya ne.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp