Home Labarai Tsaro :Jirgin Sojin Sama ya Halaka Yara 6 a Jihar Niger

Tsaro :Jirgin Sojin Sama ya Halaka Yara 6 a Jihar Niger

Gwamnatin Jihar Niger ta tabbatar da mutuwar kananan yara 6 sakamakon wani hari da Rundunar Sojin Saman Nijeriya ta kai bisa kuskure.

Sakataren Gwamnatin Jihar, Ibrahim Matane ne ya bayyana mutuwar yaran, sakamakon harin jirgin saman. Inda yace lamarin ya auku ne makon daya gabata, inda bincike ya tabbatar da cewa yaran sun halaka ne sakamakon wani hari da dakarun sojin suka kai maboyar ‘yan Bindiga a jihar.

Lamarin dai ya faru ne a garin Kurebe dake karamar hukumar shiroro ta jihar Niger.

Ko da aka tambaye shi kan mutuwar yaran 6, cewa ko dai Dakarun Sojin Saman ne suka hallaka su: yace “ hakan zai iya kasancewa, don haka ne ma gwamnatin ke sake fadada bincike kan lamarin domin tabbatar da zahirin abinda ya faru.

A cewar shugaban kungiyar gamayyar kungiyoyin Karamar Hukumar ta Shiroro Salis Sambo, yayin da yake ganawa da manema labarai, yace Dakarun Sojin sun halaka yaran ne a kokarin da suke na tarwatsa ‘Yan Ta’adda wadanda suka gudu cikin al’umma domin tsira da rayuwar su.

Yace Kananan Yaran na kan hanyar su ta dawowa daga diban ruwa a wani gulmi, inda yace hudu cikin su ‘yan gida daya ne.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp