Home Labarai Tsaro :Jirgin Sojin Sama ya Halaka Yara 6 a Jihar Niger

Tsaro :Jirgin Sojin Sama ya Halaka Yara 6 a Jihar Niger

Gwamnatin Jihar Niger ta tabbatar da mutuwar kananan yara 6 sakamakon wani hari da Rundunar Sojin Saman Nijeriya ta kai bisa kuskure.

Sakataren Gwamnatin Jihar, Ibrahim Matane ne ya bayyana mutuwar yaran, sakamakon harin jirgin saman. Inda yace lamarin ya auku ne makon daya gabata, inda bincike ya tabbatar da cewa yaran sun halaka ne sakamakon wani hari da dakarun sojin suka kai maboyar ‘yan Bindiga a jihar.

Lamarin dai ya faru ne a garin Kurebe dake karamar hukumar shiroro ta jihar Niger.

Ko da aka tambaye shi kan mutuwar yaran 6, cewa ko dai Dakarun Sojin Saman ne suka hallaka su: yace “ hakan zai iya kasancewa, don haka ne ma gwamnatin ke sake fadada bincike kan lamarin domin tabbatar da zahirin abinda ya faru.

A cewar shugaban kungiyar gamayyar kungiyoyin Karamar Hukumar ta Shiroro Salis Sambo, yayin da yake ganawa da manema labarai, yace Dakarun Sojin sun halaka yaran ne a kokarin da suke na tarwatsa ‘Yan Ta’adda wadanda suka gudu cikin al’umma domin tsira da rayuwar su.

Yace Kananan Yaran na kan hanyar su ta dawowa daga diban ruwa a wani gulmi, inda yace hudu cikin su ‘yan gida daya ne.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp