Home Taska Ministan Sadarwa ya Jagoranci Bikin Tunawa da Ranar Ƙere-Ƙere ta Duniya

Ministan Sadarwa ya Jagoranci Bikin Tunawa da Ranar Ƙere-Ƙere ta Duniya

Kashifu fo

Ministan Sadarwa ya Jagoranci Bikin Tunawa da Ranar Ƙere-Ƙere ta Duniya

Mai girma ministan sadarwa da tattalin arziƙin fasahar zamani, Farfesa Isah Ali Ibrahim Pantami, (FNCS, FBCS, FIIM), ya jagoranci bikin tunawa da zagayowar ranar nazari da ƙirƙira ta Duniya wanda hukumar bunƙasa fasahar sadarwar zamani ta ƙasa, (NITDA), ƙarƙashin jagorancin Malam Kashif Inuwa, CCIE ta shirya.

Bikin na bana wanda aka yi wa take da: Nazari da ƙirƙira na matsayin bunƙasa haɗin gwiwa domin ɗorewar tattalin arziƙin zamani”, an gudanar da shi ne a cibiyar ƙere-ƙeren kayayyakin fasahar zamani ta ƙasa (NCAIR) wacce hukumar ta (NITDA) ta samar a Abuja.

Ranar Nazari da Ƙirƙira ta Duniya rana ce da aka ware domin wayar da kai gami da zaburar da al’umma muhimmancin ƙirƙiro da abubuwa na fasahar zamani waɗanda za su zama mafita kan wata matsala a fannoni daban-daban na rayuwar jama’a daida da tanadin shirin muradi mai ɗorewa na majalisar ɗinkin duniya (UN).

A bikin na bana da ya gudana a wannan rana, mai girma shugaban hukumar ta (NITDA), ya wakilci mai girma ministan na sadarwa wajen miƙa lambobin yabo da kyaututtukan kuɗi ga gwarazan da su ka yi nasarar lashe gasar ƙere-ƙeren inda na ɗaya ya samu kyautar Naira Miliyan Biyu, na biyu ya samu kyautar Naira Miliyan Ɗaya da Dubu Ɗari Biyar, Na Uku Naira Miliyan Ɗaya, sai na Huɗu ya samu kyautar Naira Dubu Ɗari Biyar, kamar yadda aka wallafa a shafin hukumar ta (NITDA) a wannan rana.

Alhamis, 21 ga watan Afrelu, 2022.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp