Home Labarai Gwamnatin Jihar Niger ta Tabbatar da Halaka ‘Yan Bindiga a Garin Shiroro

Gwamnatin Jihar Niger ta Tabbatar da Halaka ‘Yan Bindiga a Garin Shiroro

 

Wani rahoto ya bayyana cewa, hankalin Gwamnatin jihar Niger ya kai kan wani labari da ake yadawa a kafar sada zumunta ta zamani da sauran kafafen sadarwa, cewa wani harin Jami’an tsaro ta sama yayi sanadiyyar mutuwar wasu fararen hula a garin Kurebe dake Karamar Hukumar Shiroro a Jihar.

Wannan na cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun Kwamishinan Kananan Hukumomi da masarautu na jihar Emmanuel Umar, wadda aka aikewa PRNigeria.

Sanarwar tace Gwamnatin jihar ta bayyana cewa a iyaka sanin ta babu wani farar hula daya rasa ransa sakamakon harin, haka kuma babu wani mazaunin garin da aka tilastawa shiga ko zuwa neman abinda zai ci a sansanin ‘ya gudun hijira a jihohi makotan jihar.

Gwamnatin Jihar ta Niger ta yi maraba da matakin kakkabe ‘Yan ta’adda da Rundunar Sojin Nijeriya ta dauka a  jihohin dake makotaka da jihar, da wasu kananan hukumomin jihar ciki harda kananan hukumomin Shiroro, Munya da sauran sun, matakin da yayi sanadiyyar kawar da ‘yan ta’adda masu tarin yawa a yankin.

Sanarwar tace gwamnatin jihar tayi matukar farin ciki da wannan  atisayen sakamakon nasarar da yake samu na halaka ‘yan bindiga a kananan hukumomin da lamarin ya shafa, wannan hadakar ta taimaka matuka wajen dakile ayyukan ‘yan ta’addan a kanana hukumomin Munya da Shiroro, tare da kubutar da wasu mutane da dama.

Daga bisani Gwamnatin Jihar ta nuna jindadin bisa nasarar da dakarun hadin Gwuiwar ke samu, tare da karin karfin gwuiwar cigaba da kakkabe su daga cikin Al’ummar dake yankin, domin su sami damar komawa gonakin su da cigaba da ayyukan su na yau da kullum.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp