Home Labarai Gwamnatin Jihar Niger ta Tabbatar da Halaka ‘Yan Bindiga a Garin Shiroro

Gwamnatin Jihar Niger ta Tabbatar da Halaka ‘Yan Bindiga a Garin Shiroro

 

Wani rahoto ya bayyana cewa, hankalin Gwamnatin jihar Niger ya kai kan wani labari da ake yadawa a kafar sada zumunta ta zamani da sauran kafafen sadarwa, cewa wani harin Jami’an tsaro ta sama yayi sanadiyyar mutuwar wasu fararen hula a garin Kurebe dake Karamar Hukumar Shiroro a Jihar.

Wannan na cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun Kwamishinan Kananan Hukumomi da masarautu na jihar Emmanuel Umar, wadda aka aikewa PRNigeria.

Sanarwar tace Gwamnatin jihar ta bayyana cewa a iyaka sanin ta babu wani farar hula daya rasa ransa sakamakon harin, haka kuma babu wani mazaunin garin da aka tilastawa shiga ko zuwa neman abinda zai ci a sansanin ‘ya gudun hijira a jihohi makotan jihar.

Gwamnatin Jihar ta Niger ta yi maraba da matakin kakkabe ‘Yan ta’adda da Rundunar Sojin Nijeriya ta dauka a  jihohin dake makotaka da jihar, da wasu kananan hukumomin jihar ciki harda kananan hukumomin Shiroro, Munya da sauran sun, matakin da yayi sanadiyyar kawar da ‘yan ta’adda masu tarin yawa a yankin.

Sanarwar tace gwamnatin jihar tayi matukar farin ciki da wannan  atisayen sakamakon nasarar da yake samu na halaka ‘yan bindiga a kananan hukumomin da lamarin ya shafa, wannan hadakar ta taimaka matuka wajen dakile ayyukan ‘yan ta’addan a kanana hukumomin Munya da Shiroro, tare da kubutar da wasu mutane da dama.

Daga bisani Gwamnatin Jihar ta nuna jindadin bisa nasarar da dakarun hadin Gwuiwar ke samu, tare da karin karfin gwuiwar cigaba da kakkabe su daga cikin Al’ummar dake yankin, domin su sami damar komawa gonakin su da cigaba da ayyukan su na yau da kullum.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp