Home Labarai Gwamnatin Jihar Niger ta Tabbatar da Halaka ‘Yan Bindiga a Garin Shiroro

Gwamnatin Jihar Niger ta Tabbatar da Halaka ‘Yan Bindiga a Garin Shiroro

 

Wani rahoto ya bayyana cewa, hankalin Gwamnatin jihar Niger ya kai kan wani labari da ake yadawa a kafar sada zumunta ta zamani da sauran kafafen sadarwa, cewa wani harin Jami’an tsaro ta sama yayi sanadiyyar mutuwar wasu fararen hula a garin Kurebe dake Karamar Hukumar Shiroro a Jihar.

Wannan na cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun Kwamishinan Kananan Hukumomi da masarautu na jihar Emmanuel Umar, wadda aka aikewa PRNigeria.

Sanarwar tace Gwamnatin jihar ta bayyana cewa a iyaka sanin ta babu wani farar hula daya rasa ransa sakamakon harin, haka kuma babu wani mazaunin garin da aka tilastawa shiga ko zuwa neman abinda zai ci a sansanin ‘ya gudun hijira a jihohi makotan jihar.

Gwamnatin Jihar ta Niger ta yi maraba da matakin kakkabe ‘Yan ta’adda da Rundunar Sojin Nijeriya ta dauka a  jihohin dake makotaka da jihar, da wasu kananan hukumomin jihar ciki harda kananan hukumomin Shiroro, Munya da sauran sun, matakin da yayi sanadiyyar kawar da ‘yan ta’adda masu tarin yawa a yankin.

Sanarwar tace gwamnatin jihar tayi matukar farin ciki da wannan  atisayen sakamakon nasarar da yake samu na halaka ‘yan bindiga a kananan hukumomin da lamarin ya shafa, wannan hadakar ta taimaka matuka wajen dakile ayyukan ‘yan ta’addan a kanana hukumomin Munya da Shiroro, tare da kubutar da wasu mutane da dama.

Daga bisani Gwamnatin Jihar ta nuna jindadin bisa nasarar da dakarun hadin Gwuiwar ke samu, tare da karin karfin gwuiwar cigaba da kakkabe su daga cikin Al’ummar dake yankin, domin su sami damar komawa gonakin su da cigaba da ayyukan su na yau da kullum.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp