Home Taska Hukumar NITDA ta Kammala ba da Horon Kwarewa ga Jami’an Gwamnati

Hukumar NITDA ta Kammala ba da Horon Kwarewa ga Jami’an Gwamnati

Certificate

Hukumar NITDA ta Kammala ba da Horon Kwarewa ga Jami’an Gwamnati

A ƙoƙarin da ta ke cigaba da yi wajen horar da ƴan ƙasa, gami da bunƙasa ilimin jami’an gwamnatin tarayya kan amfani da fasahar zamani, hukumar bunƙasa fasahar sadarwar zamani ta ƙasa (NITDA), ƙarƙashin jagorancin Malam Kashif Inuwa Abdullahi, (CCIE), da ke ƙarƙashin kulawar ma’aikatar sadarwa da tattalin arziƙin fasahar zamani, ƙarƙashin jagorancin Farfesa Isah Ali Ibrahim Pantami, (FNCS, FBCS, FIIM), ta kammala ba da horon bunƙasa ƙwarewa kan amfani da fasahar zamani ga jami’an gwamnatin tarayya.

Jami’an gwamnatin waɗanda su ka fito daga hukumomin tsaro da sauran sassan ma’aikatu da hukumomin gwamnatin tarayya, an ba su horon ƙwarewar akan harkokin tsaro na yanar gizo-gizo da sarrafa na’ura mai ƙwaƙwalwa.

Jim kaɗan da kammala horon a wannan rana, mai girma shugaban hukumar ta (NITDA), Malam Kashif Inuwa Abdullahi, (CCIE) wanda Dakta Usman Gambo Abdullahi, shugaban sashen warware matsalolin ayyukan fasahar zamani na hukumar ya wakilta, ya miƙawa waɗanda aka horar ɗin takardunsu na shaidar samun horon, a cibiyar horar da ma’aikata da ke yankin Kubwa a birnin tarayya, Abuja.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp