Home Taska Hukumar NITDA ta Kammala ba da Horon Kwarewa ga Jami’an Gwamnati

Hukumar NITDA ta Kammala ba da Horon Kwarewa ga Jami’an Gwamnati

Certificate

Hukumar NITDA ta Kammala ba da Horon Kwarewa ga Jami’an Gwamnati

A ƙoƙarin da ta ke cigaba da yi wajen horar da ƴan ƙasa, gami da bunƙasa ilimin jami’an gwamnatin tarayya kan amfani da fasahar zamani, hukumar bunƙasa fasahar sadarwar zamani ta ƙasa (NITDA), ƙarƙashin jagorancin Malam Kashif Inuwa Abdullahi, (CCIE), da ke ƙarƙashin kulawar ma’aikatar sadarwa da tattalin arziƙin fasahar zamani, ƙarƙashin jagorancin Farfesa Isah Ali Ibrahim Pantami, (FNCS, FBCS, FIIM), ta kammala ba da horon bunƙasa ƙwarewa kan amfani da fasahar zamani ga jami’an gwamnatin tarayya.

Jami’an gwamnatin waɗanda su ka fito daga hukumomin tsaro da sauran sassan ma’aikatu da hukumomin gwamnatin tarayya, an ba su horon ƙwarewar akan harkokin tsaro na yanar gizo-gizo da sarrafa na’ura mai ƙwaƙwalwa.

Jim kaɗan da kammala horon a wannan rana, mai girma shugaban hukumar ta (NITDA), Malam Kashif Inuwa Abdullahi, (CCIE) wanda Dakta Usman Gambo Abdullahi, shugaban sashen warware matsalolin ayyukan fasahar zamani na hukumar ya wakilta, ya miƙawa waɗanda aka horar ɗin takardunsu na shaidar samun horon, a cibiyar horar da ma’aikata da ke yankin Kubwa a birnin tarayya, Abuja.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp