Ta cikin wata ganawa da sukayi da shugaban kasa muhammadu Buhari, Gwamnonin, sun jaddada aniyar sun a mayar da mulkin Kudancin kasar a shekarar 2023
Shugaban kungiyar Gwamnonin kuma gwamnan jihar Plateau Simon lalong, ne ya bayyana hakan ga manema labarai jim kadan bayan ganawar a fadar shugana kasa dake Villa a babban birnin tarayyar Nijeriya, inda yace shugaba Buhari ya tabbatar musu cewa bai goyi bayan wani mutum ba cikin mutum 23 da ke son jam’iyyar ta tsayar da su Takara.
Read Also:
Shi ma da yake jawabi, shugaban kungiyar gwamnonin APC kuma gwamnan Jihar Kebbi, Atiku Bagudu, ya ce sun dauki matakin goyon bayan dan takara daga kudancin kasar ne domin tabbatar da adalci da zaman lafiya a kasar.
Dambarwar da ake yi kan batun dan takarar shugaban kasar na Najeriya a jam’iyyar APC ta sa shugaban kasar Muhammadu Buhari ya fitar da sanarwa yana nesanta kansa ga goya wa kowanne dan takara baya.
Wannan kuma na kunshe ta cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasar, Malam Garba Shehu ya aike wa manema labarai inda ya ambato Shugaba Buhari yana cewa babu wanda ya zaba a matsayin dan takarar APC na shugaban kasa a zaben 2023.












