Home SIYASA Gwamnonin Arewacin Nijeriyar sun yi Fatali Da Zabin Lawan Matsayin Dan Takarar...

Gwamnonin Arewacin Nijeriyar sun yi Fatali Da Zabin Lawan Matsayin Dan Takarar APC

Ta cikin wata ganawa da sukayi da shugaban kasa muhammadu Buhari, Gwamnonin, sun jaddada aniyar sun a mayar da mulkin Kudancin kasar a shekarar 2023

Shugaban kungiyar Gwamnonin kuma gwamnan jihar Plateau Simon lalong, ne ya bayyana hakan ga manema labarai jim kadan bayan ganawar a fadar shugana kasa dake Villa a babban birnin tarayyar Nijeriya, inda yace shugaba Buhari ya tabbatar musu cewa bai goyi bayan wani mutum ba cikin mutum 23 da ke son jam’iyyar ta tsayar da su Takara.

Shi ma da yake jawabi, shugaban kungiyar gwamnonin APC kuma gwamnan Jihar Kebbi, Atiku Bagudu, ya ce sun dauki matakin goyon bayan dan takara daga kudancin kasar ne domin tabbatar da adalci da zaman lafiya a kasar.

Dambarwar da ake yi kan batun dan takarar shugaban kasar na Najeriya a jam’iyyar APC ta sa shugaban kasar Muhammadu Buhari ya fitar da sanarwa yana nesanta kansa ga goya wa kowanne dan takara baya.

Wannan kuma na kunshe ta cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasar, Malam Garba Shehu ya aike wa manema labarai inda ya ambato Shugaba Buhari yana cewa babu wanda ya zaba a matsayin dan takarar APC na shugaban kasa a zaben 2023.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp