Home Labarai Yadda Iyalan Sheik Agaka Suka Bawa Iyalai Na Ilimin Addinin Musulunci, “Sulu...

Yadda Iyalan Sheik Agaka Suka Bawa Iyalai Na Ilimin Addinin Musulunci, “Sulu Gambari”

Mai Martaba Sarkin Ilorin, Alhaji Ibrahim Sulu Gambari, ya bayyana Marigayi Dr. Abdulhameed Shuaib Agaka matsayin mai kyakkyawan halaye da riko da addini.

Sheik Agaka, Mahaifi ga mawallafin jaridar PRNigeria kuma babban mai tace labarai, Yusha’u Shuaib, ya rasu a ranar Asabar, yana da shekaru 77 a duniya.

Agaka fitacce malamin Addinin muslunci kuma babban limamin garin Agaka dake masarautar Ilorin ta Jihar Kwara, ya rasu ne a wani asibiti mai zaman kansa dake garin, bayan yayi fama da gajeruwar rashin lafiya.

Haka zalika yana da digirin digirgir a fannin falsafa, an haife shi a cikin dangin Imam Shuaib Saeed, wani mashahurin malami masanin Al’kurani kuma jagoran addini musulunci.

Mai Martaba sarkin Ilorin Sulu Gambari ya bayyana matukar kaduwarsa bisa ga rasuwar mahaifin mawallafin jaridar ta PRNigeria, yayi da ya karbi bakuncin tawagar Iyalan marigayin, a fadarsa, a ranar litinin.

Mai martaba sarkin ya kuma jajantawa tawagar iyalan marigayin bisa jagorancin Dawudu Agaka, Alh. Hanafi Folorunsho Kawu, da daukacin  iyalan Malamin bisa rashin da suka yi na hazaki, kuma cikakken Mutum mai adalci marashin aibi.

Sarkin bayyana cewa Al’ummar jihar kwara da kasa baki daya sunyi gagarumin rashi na malamin Addini da baza a iya misalta rashin ba.

Sarkin na Ilorin ya kara da cewa Iyalan Sheik Agaka, na da alaka da masu yawon yada addinin Musulunci “masu wa’azi” tsawon shekaru da dama a Nijeriya, kasancewar marigayu Abdulhameed ya kasance daya daga cikin manayan malaman addinin muslunci da masarautar ta samar.

Dr. Sulu Gambari, yace ya amfana matuka da wa’azin sheik Abduhameed, inda yace mahaifiyar sa ta kuma shafe shekarunta tana karatu al’kurani a wajen Sheik Agaka.

Tun bayan samun labarin mutuwar Sheik Agaka manayan malamai gami da masu rike da sarautun gargaji, da ‘yan takarda sun nuna kaduwar su matuka tare da Addu’ar Allah yayi masa rahama yasa Aljanna ce makoma ya kuma inganta abinda ya bari.

By PRNigeria

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp