Home Labarai Yadda Iyalan Sheik Agaka Suka Bawa Iyalai Na Ilimin Addinin Musulunci, “Sulu...

Yadda Iyalan Sheik Agaka Suka Bawa Iyalai Na Ilimin Addinin Musulunci, “Sulu Gambari”

Mai Martaba Sarkin Ilorin, Alhaji Ibrahim Sulu Gambari, ya bayyana Marigayi Dr. Abdulhameed Shuaib Agaka matsayin mai kyakkyawan halaye da riko da addini.

Sheik Agaka, Mahaifi ga mawallafin jaridar PRNigeria kuma babban mai tace labarai, Yusha’u Shuaib, ya rasu a ranar Asabar, yana da shekaru 77 a duniya.

Agaka fitacce malamin Addinin muslunci kuma babban limamin garin Agaka dake masarautar Ilorin ta Jihar Kwara, ya rasu ne a wani asibiti mai zaman kansa dake garin, bayan yayi fama da gajeruwar rashin lafiya.

Haka zalika yana da digirin digirgir a fannin falsafa, an haife shi a cikin dangin Imam Shuaib Saeed, wani mashahurin malami masanin Al’kurani kuma jagoran addini musulunci.

Mai Martaba sarkin Ilorin Sulu Gambari ya bayyana matukar kaduwarsa bisa ga rasuwar mahaifin mawallafin jaridar ta PRNigeria, yayi da ya karbi bakuncin tawagar Iyalan marigayin, a fadarsa, a ranar litinin.

Mai martaba sarkin ya kuma jajantawa tawagar iyalan marigayin bisa jagorancin Dawudu Agaka, Alh. Hanafi Folorunsho Kawu, da daukacin  iyalan Malamin bisa rashin da suka yi na hazaki, kuma cikakken Mutum mai adalci marashin aibi.

Sarkin bayyana cewa Al’ummar jihar kwara da kasa baki daya sunyi gagarumin rashi na malamin Addini da baza a iya misalta rashin ba.

Sarkin na Ilorin ya kara da cewa Iyalan Sheik Agaka, na da alaka da masu yawon yada addinin Musulunci “masu wa’azi” tsawon shekaru da dama a Nijeriya, kasancewar marigayu Abdulhameed ya kasance daya daga cikin manayan malaman addinin muslunci da masarautar ta samar.

Dr. Sulu Gambari, yace ya amfana matuka da wa’azin sheik Abduhameed, inda yace mahaifiyar sa ta kuma shafe shekarunta tana karatu al’kurani a wajen Sheik Agaka.

Tun bayan samun labarin mutuwar Sheik Agaka manayan malamai gami da masu rike da sarautun gargaji, da ‘yan takarda sun nuna kaduwar su matuka tare da Addu’ar Allah yayi masa rahama yasa Aljanna ce makoma ya kuma inganta abinda ya bari.

By PRNigeria

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp