Home General Zaman Gida: Mayakan IPOB Sun Kone Motar Siminti a Jihar Enugu

Zaman Gida: Mayakan IPOB Sun Kone Motar Siminti a Jihar Enugu

‘Yan bindiga da ake zargin mambobin haramtacciyar kungiyar ‘yan awaren biyafara ce dake gudanar da ayyukan ta a Kudu Maso Gabashin Nijeriya, a wani bangare na tabbatar da kudirin zaman gida dole ga Al’ummar yankin sun kone Motar siminti ta Dangote makare da kaya a mahadar Beach dake karamar hukumar Nsukka dake Jihar Enugu kasar.

Wasu mazauna yankin da suka bukaci a sakaye sunansu, sun bayyana cewa lamarin ya auku ne da misalin karfe 5:30 na Asubahi inda Al’ummar yankin ke tsaka da bacci.

Duk da dai ba’a rasa rai ba amma dai an rawaito cewa maharan sun lakadawa matukin motar dukan kawo wuka, inda daga bisani suka kuma sakeshi ya tafi.

“Na ji kukan wani wanda daga bisani na fahimci direban motar ne. Abu na gaba da na gani kuma shine hayaki na tashi daga motar, wanda ke alamta a kunna mata wuta, kamar yadda majiyar ta tabbatar, a cewar wani mazaunin yankin.

PRNigeria ta rawaito cewa bayan sun bar wajen ne wasu daga cikin Al’umma suka kashe wutar domin hana cinye motar, kasancewar motar na dauke da simintin na miliyoyin Naira.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp