Home General Zaman Gida: Mayakan IPOB Sun Kone Motar Siminti a Jihar Enugu

Zaman Gida: Mayakan IPOB Sun Kone Motar Siminti a Jihar Enugu

‘Yan bindiga da ake zargin mambobin haramtacciyar kungiyar ‘yan awaren biyafara ce dake gudanar da ayyukan ta a Kudu Maso Gabashin Nijeriya, a wani bangare na tabbatar da kudirin zaman gida dole ga Al’ummar yankin sun kone Motar siminti ta Dangote makare da kaya a mahadar Beach dake karamar hukumar Nsukka dake Jihar Enugu kasar.

Wasu mazauna yankin da suka bukaci a sakaye sunansu, sun bayyana cewa lamarin ya auku ne da misalin karfe 5:30 na Asubahi inda Al’ummar yankin ke tsaka da bacci.

Duk da dai ba’a rasa rai ba amma dai an rawaito cewa maharan sun lakadawa matukin motar dukan kawo wuka, inda daga bisani suka kuma sakeshi ya tafi.

“Na ji kukan wani wanda daga bisani na fahimci direban motar ne. Abu na gaba da na gani kuma shine hayaki na tashi daga motar, wanda ke alamta a kunna mata wuta, kamar yadda majiyar ta tabbatar, a cewar wani mazaunin yankin.

PRNigeria ta rawaito cewa bayan sun bar wajen ne wasu daga cikin Al’umma suka kashe wutar domin hana cinye motar, kasancewar motar na dauke da simintin na miliyoyin Naira.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp