Home Labarai Dakarun Sojin Sama Sun Halaka Mayakan ISWAP 13 Tare da Kama 5

Dakarun Sojin Sama Sun Halaka Mayakan ISWAP 13 Tare da Kama 5

Dakarun sojin saman Nijeriya sun sami nasarar halaka mayakan kungiyar Boko Haram tsagin ISWAP, a yakin Arewa Maso Gabashin kasar kamar yadda PRNigeria ta rawaito.

Mayakan da dakarun suka halaka da sanyin safiyar Litinin sun sanya shingen tsare ababa hawa a hanyar  Goni Masari dake kusa da hanayar Maiduguri zuwa Damaturu, a jihar Borno.

Dakarun rundunar sojin  sun sami wani rahoton sirri daya bayyana yadda mayakan suka tare kan hanyar wanda tuni har sun sami damar yin garkuwa da wani matukin mota, nan basuyi kasa a gwuiwa ba suka farmake su da jiragen yaki.

A cewar kwmandan daya jagoranci kai harin yace dakarun sojin sun sami nasarar kubutar da wanda akayi garkuwa dasu su 5, a harin da suka kai wa ‘yan ta’addan.

Kwamandan, wanda ya ki bayyana sunansa ga PRNigeria, yace sojojin sun halaka mayakan kungiyar ta ISWAP sama da 13, tare da raunata wasu da dama, inda suka sami nasarar kwato motar dake dauke da bindiga da suka bari a wajen.

By PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp