Home Labarai Dakarun Sojin Sama Sun Halaka Mayakan ISWAP 13 Tare da Kama 5

Dakarun Sojin Sama Sun Halaka Mayakan ISWAP 13 Tare da Kama 5

Dakarun sojin saman Nijeriya sun sami nasarar halaka mayakan kungiyar Boko Haram tsagin ISWAP, a yakin Arewa Maso Gabashin kasar kamar yadda PRNigeria ta rawaito.

Mayakan da dakarun suka halaka da sanyin safiyar Litinin sun sanya shingen tsare ababa hawa a hanyar  Goni Masari dake kusa da hanayar Maiduguri zuwa Damaturu, a jihar Borno.

Dakarun rundunar sojin  sun sami wani rahoton sirri daya bayyana yadda mayakan suka tare kan hanyar wanda tuni har sun sami damar yin garkuwa da wani matukin mota, nan basuyi kasa a gwuiwa ba suka farmake su da jiragen yaki.

A cewar kwmandan daya jagoranci kai harin yace dakarun sojin sun sami nasarar kubutar da wanda akayi garkuwa dasu su 5, a harin da suka kai wa ‘yan ta’addan.

Kwamandan, wanda ya ki bayyana sunansa ga PRNigeria, yace sojojin sun halaka mayakan kungiyar ta ISWAP sama da 13, tare da raunata wasu da dama, inda suka sami nasarar kwato motar dake dauke da bindiga da suka bari a wajen.

By PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp