Home Taska Ambaliyar Ruwa a Jigawa: Gidauniyar Ƙasar Qatar da ta Malam Inuwa Sun...

Ambaliyar Ruwa a Jigawa: Gidauniyar Ƙasar Qatar da ta Malam Inuwa Sun Raba Tallafin Abinci ga Mutane 1,000

Tallafi

Ambaliyar Ruwa a Jigawa: Gidauniyar Ƙasar Qatar da ta Malam Inuwa Sun Raba Tallafin Abinci ga Mutane 1,000

 

Biyo bayan iftila’in ambaliyar ruwa da ta afkawa al’ummar Jihar Jigawa a bara, gidauniyar ba da agaji ta Duniya, (Qatar Charity Foundation) da haɗin gwiwar (Gidauniyar Malam Inuwa) ta mai girma shugaban hukumar bunƙasa fasahar sadarwar zamani ta ƙasa, (NITDA), Malam Kashifu Inuwa Abdullahi, (CCIE), sun raba tallafin kayan abinci ga mutane (1,000) daga cikin mutanen da iftila’in ambaliyar ta shafa.

Rabon kayan wanda aka ƙaddamar da shi yau a ofishin gidauniyar da ke kan titin Garun-Gabas, a ƙaramar hukumar Haɗejia, an rabawa mutane (600) nasu waɗanda aka zaƙulo daga ƙananan hukumomi takwas da ke yanƙin ƙasar Haɗejia inda daga bisani za a rabawa sauran yankunan.

Da ya ke bayani jim kaɗan bayan kammala rabon, shugaban gidauniyar Malam Inuwa, Dakta Hussaini Yusuf Baban ya bayyana cewa an warewa yankin ƙasar Haɗejia kason mutum ɗari shida ne duba da girman annobar a yankin.

Da ya ke tsokaci dangane da hanyoyin da su ka bi wajen zaƙulowa gami da tantance mutanen da su ka amfana da tallafin kuwa, Dakta Baban ya bayyana cewa: “Mun tuntuɓi shugabannin ƙananan hukumomi haɗi da Limamai da kuma amintattun mutane wajen haɗa sunayen. Kuma duk wanda mu ka ba wa wannan tallafi ɗaya ne daga cikin mutanen da ruwa ya yi wa ɓarna in ma a gida ko a gona,”. Inji shugaban gidauniyar.

Kayayyakin da aka raba ɗin sun haɗa da: Taliya, Shinkafa, Semovita, wake da Mai. Mutanen da su ka amfanan sun yi godiya haɗi da addu’ar fatan alkhairi ga gidauniyoyin biyu bisa tallafin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp