Home General Hukumar zabe tace a shirye take wajen gudanar da zaben 2023

Hukumar zabe tace a shirye take wajen gudanar da zaben 2023

Shugaban Hukumar Zaben Najeriya Farfesa Mahmood Yakub ya ce za a gudanar da zabukan kasar da ke tafe kamar yadda aka tsara a wannan shekara ta 2023.

Yayin da yake jawabi a taron majalisar zartarwar kasar da Shugaba Muhammadu Buhari ya jagoranta yau Laraba a fadar mulki da ke Abuja, Mahmood ya ce zaben shugaban kasa da ‘yan majalisar tarayya yana nan yadda aka tsara ranar 25 ga watan nan na Fabrairu.

Haka kuma shi ma zaben gwamnoni da na ‘yan majalisar jihohi da za a yi ranar 11 ga watan Maris yana nan ba ja da baya kamar yadda aka tsara yi, in ji shugaban na INEC.

Shugaban hukumar zaben ya bayyana gaban majalisar ne yayin da ya rage kwana 17 a fara zabukan, domin ya yi bayani kan halin da ake ciki game da shirye-shiryen hukumarsa.

Da yake zantawa da manema labarai bayan fitowa daga zauren majalisar, Farfesa Yakubu ya ce ya bayyana ne gaban majalisar ministocin domin sanar da ita irin shirin da hukumar ta yi na gudanar da manyan zabukan na bana.

Ya kara da cewa daman abin da aka saba yi ne a duk lokacin da ake daf da zabe a kasar, shugaban hukumar ya yi wa majalisar zartawa bayani inda shirye-shiryen suka kwana.

Sai dai akwai wasu matsaloli guda uku da a baya hukumar ta ce ka iya yin tarnaki ga gudanar zabukan, matsalolin da suka kunshi rashin tsaro da karancin takardun kudi da kuma man fetur.

Ko baya ga yin wannan bahasin gaban majalisar ministocin, ana sa ran shugaban hukumar zaben ya sake bayyana gaban majalisar magabata ta kasa wato Council of State ranar Juma’a, domin sanar da ita a hukumance irin yadda hukumarsa ta kintsa domin gudanar da manyan zabukan.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp