Home General Hukumar zabe tace a shirye take wajen gudanar da zaben 2023

Hukumar zabe tace a shirye take wajen gudanar da zaben 2023

Shugaban Hukumar Zaben Najeriya Farfesa Mahmood Yakub ya ce za a gudanar da zabukan kasar da ke tafe kamar yadda aka tsara a wannan shekara ta 2023.

Yayin da yake jawabi a taron majalisar zartarwar kasar da Shugaba Muhammadu Buhari ya jagoranta yau Laraba a fadar mulki da ke Abuja, Mahmood ya ce zaben shugaban kasa da ‘yan majalisar tarayya yana nan yadda aka tsara ranar 25 ga watan nan na Fabrairu.

Haka kuma shi ma zaben gwamnoni da na ‘yan majalisar jihohi da za a yi ranar 11 ga watan Maris yana nan ba ja da baya kamar yadda aka tsara yi, in ji shugaban na INEC.

Shugaban hukumar zaben ya bayyana gaban majalisar ne yayin da ya rage kwana 17 a fara zabukan, domin ya yi bayani kan halin da ake ciki game da shirye-shiryen hukumarsa.

Da yake zantawa da manema labarai bayan fitowa daga zauren majalisar, Farfesa Yakubu ya ce ya bayyana ne gaban majalisar ministocin domin sanar da ita irin shirin da hukumar ta yi na gudanar da manyan zabukan na bana.

Ya kara da cewa daman abin da aka saba yi ne a duk lokacin da ake daf da zabe a kasar, shugaban hukumar ya yi wa majalisar zartawa bayani inda shirye-shiryen suka kwana.

Sai dai akwai wasu matsaloli guda uku da a baya hukumar ta ce ka iya yin tarnaki ga gudanar zabukan, matsalolin da suka kunshi rashin tsaro da karancin takardun kudi da kuma man fetur.

Ko baya ga yin wannan bahasin gaban majalisar ministocin, ana sa ran shugaban hukumar zaben ya sake bayyana gaban majalisar magabata ta kasa wato Council of State ranar Juma’a, domin sanar da ita a hukumance irin yadda hukumarsa ta kintsa domin gudanar da manyan zabukan.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp