Home General Kungiyar Makarfi Ambassadors tayi Allawadai da hukuncin da kotun koli ta ‘yanke...

Kungiyar Makarfi Ambassadors tayi Allawadai da hukuncin da kotun koli ta ‘yanke kan shari’a Machina da Ahmad Lawan

Kungiyar Makarfi Ambassadors ta bayyana hukuncin da kotun koli ta ‘yanke kan shari’a Machina da Ahmad Lawan matsayin rashin adalci

Kungiyar wacce kungiya ce dake goyon bayan babbar jam’iyyar hamayya ta Nijeriya PDP, wanda tace ta lura cewa alkalai uku na kotun da suka yi watsi da hukunce-hukuncen farko na babbar kotun tarayya da kotun daukaka kara ba su taimaka wa dimokradiyyar kasar ba.
Kungiyar tace, wannan hukunci ba abin razanarwa bane kai dai, lamari ne marasa dadi ga damukradiyya.
A ranar litinin din data gabata ne kotun kolin kasar ta yanke hukunci kan shari’ar dake tsakanin shugaban majalisar dattawa da Bashir Machina, bisa sahihancin wanda ya kamata ya yiwa jam’iyyar sa ta APC takarar wakilcin yankin Yobe ta Arewa, hukunci da ake kallon an yiwa Ahmad lawan Alfarma a cikin sa.
Tunda fari dai kuton Tarayya a Damaturu da kotun daukaka kara da ke Abuja sun yanke hukuncin daya bawa Machina nasara.
Da take mayara da martani ta cikin wata takardar sanarwa mai dauke da sa hannun kodinetan kungiyar kan al’amurra na musamman Mr. Abdullahi Ahmad da kodinetan shiri da tsare-tsare Engr. Bolade Aina, kungiyar ta bayyana takaicinta, inda tace Sanata Ahmad lawan bai shiga zaben fidda gwani na jam’iyyar APC da aka kudanar a jihar Yobe ba, zaben daya tabbatar da machina matsayin wanda yayi nasara.
Makarfi Ambassadors sunce “a fahimtarsu da dokokin zabe, wajibi ne dan takara ya shiga zaben fidda gwani da jam’iyyun su suka hada.
“Amma yaya tunani zai yadda da ganin an bawa wanda bai taka rawa a gas aba lambar yabo kwatankwacin wadanda suka fafata a gasa?’
“kananan kotunan da suka yanke hukunci a kan wannan Al’amari, a ganinmu, sun yi abin da ya kamata. Haka kuma Alkalan kotun Koli su 3 da suka yi watsi da hukunce-hukuncen ta bayyana karara basu taimaki damukradiyya ba.
Abinda muka dauka matsayin mataki kuma shi ne, bangaren shari’a, musamman ma koli a karkashin jam’iyyar APC mai Mulki ba zai zama mafita ta karshe ga talakawan kasar ba.
Idan dai za’a iya tunawa wani hukuncin kotin kolin makamancin wannan daya bawa Hope Uzodinma nasara wanda kuma shine na 4 a zaben da aka fafata a jihar ta Imo.
Don haka muna kira ga ‘yan Nijeriya dasu fatattaki jam’iyyar APC, ta hanyar zaben jam’iyyar Adawa ta PDP domin cancantar ta.
PDP it ace kadai jam’iyya dake mutunta doka, ta kuma nuna an gani a kasar lokacin data rike shugabancin kasar tsahon shekaru 16.
A jihar kaduna Makarfi ambassadors ta bukaci Al’ummar jihar dasu zabi Hon Isa Ashiru kudan domin ceto jihar daga halin da take ciki.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp