Home AFIRKA Rashawa na janyo wa Uganda asarar sama da dala biliyan 2 duk...

Rashawa na janyo wa Uganda asarar sama da dala biliyan 2 duk shekara

Uganda na yin asarar kuɗin da ya kai Dalar Amurka biliyan 2 da miliyan 500 a duk shekara saboda cin hancin, kwatankwacin kaso 1 bisa 4 na kasafin kuɗin da ƙasar ke yi, kamar yadda hukumar da ke yaƙar cin hanci a  ƙasar ta tabbatar.

A cewar shugabar hukumar yaƙi da cin hanci ta Uganda Beti Kamya Turwomwe, ƙasar na asarar sama da tiriliyan 9 da miliyan 100 na kuɗin ƙasar Shiling, kwatankwacin dala biliyan 2 da miliyan 500 a duk shekara.

Ta ce wannan ya kai kaso 23 cikin 100 na kasafin kuɗin ƙasar, abin da ke zama wani babban ƙalubale ga ayyukan daƙile cin hanci a ƙasar.

Cin hanci da rashawa wata gagarumar matsala ce da ke addabar gabashin Afirka.

Shugaban ƙasar Uganda Yoweri Musaveni ya sha nanata alwashin ɗaukar matakan da za su kawo ƙarshen matsalar cin hanci ganin yadda matsalar ta ratsa cikin jami’an gwamnati.

Turwomwe ta ce sashin da ta ke jagoranta ya samu nasrar ƙwato dala miliyan 2 da aka wawushe, inda ta nuna damuwa kan rashin sanya kuɗi a hukumar da take jagoranta.

Wannan kalaman nata ya biyo bayan rahoton shekara-shekara da ake fitarwa na cibiyar bincike kan tabbbatar da ganin an yi ayyukan gwamnati a buɗe babu kumbiya-kumbiya.

Rahoton na zuwa mako guda da shugaban Uganda Yoweri Musaveni ya sanar da yafewa wasu manyan jami’an gwamnati da aka ɗaue shekara 10 saboda kamasu da badaƙalar dala miliyan 1 da miliyan 200.

Musaveni ya yafe musu bayan sun kammala shekara 5 a gidan 5, abinda ya tunzura kungiyoyin fararan hula

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp