Home Labarai Maja tsakanin Kwankwaso da Obi ba za tayi nasara ba – APC

Maja tsakanin Kwankwaso da Obi ba za tayi nasara ba – APC

Jam’iyyar APC mai mulki ta ce bata tsorata ba da yunkurin kulla kawance tsakananin Rabi’u Musa Kwakwanso na NNPP da Peter Obi na LP a yayin da ake tunkarar zaben shugaban kasa na 2027.

A yayin ganawa da jaridar The PUNCH a ranar Litinin, daraktan yada labarai na APC, Bala Ibrahim ya bayyana cewa yunkurin kawance tsakanin Kwankwaso da Obi ba zai nasara ba kamar yadda ya faru a zaben 2023.

Acewarsa, rashin amincewa tsakanin Obi da Kwankwaso zai zama cikas gare su, kuma duk a cikin su ba wanda zai hakura ya bar wa wani takarar shugaban kasa.

tun da fari dai an hangi Kwankwaso na cewa bashi da matsala idan an ce ya yiwa Obi mataimaki, amma azo a duba waye ya fi chanchanta, duk da cewar dai da dama cikin jaridun Nijeriya sun yiwa kalaman nasa bahaguwar fahimta

Da yake mayar da martani a ranar Litinin, Sakataren jam’iyyar LP, Umar Faruk ya yi maraba da damar da Kwankwaso ya bayar, inda ya ce majar za ta yiwuwa idan Kwankwaso ya amince zai yi aiki da Obi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp