Rigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka – Hukumar Lafiya ta Duniya
Wani rahoto da Hukumar Lafiya ta Duniya ta fitar ya bayyana cewa allurar rigakafin ƙyanda na yara da ake yi ya ceci rayukan kusan mutum miliyan 20 a Afrika cikin shekaru 25 na ƙarnin da ya gabata.
Read Also:
Alkaluman da aka tattara tare da haɗin gwiwar shirin rigakafin GAVI, sun nuna adadin mutuwar da ake samu sakamakon cutar kyanda ya ragu a tsawon wancan lokacin.
Kasashen Cape Verde da Mauritius da Seychelles a bara sun zama kasashe na farko a yankin kudu da hamadar Sahara da suka kawar da cutar gaba daya.
Ci gaban da aka samu ya ƙara bayyana ƙoƙarin da ake yi na faɗaɗa shirye-shiryen rigakafin yara ciki har da na cututtuka kamar ciwon sanƙarau da zazzaɓin cizon sauro.
Amma masana sun yi gargaɗin cewa hallau akwai ƙalubale saboda har yanzu miliyoyin yara ba su samu allurar kariya daga cutar ba.












