Home SIYASA 2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara – Atiku

2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara – Atiku

Atiku

2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara – Atiku

 

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya Atiku Abubakar, ya ce ba zai sake neman takarar shugaban ƙasar daga 2027 ba.

Ya ce idan aka yi la’akari da shekarunsa da kuma damar da yake da ita ba lallai ya ci gaba da neman damar daga shekara mai zuwa ba.

Atiku ya bayyana hakan ne a wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin na Arise a ranar Laraba.

Da aka tambaye shi game da cikarsa shekaru 80 a shekarar 2027 da yadda hakan zai iya daƙile masa damarsa, Atiku ya ce: “Tabbas za a samu ƙarin masu nema, kuma ita ce dama ta ƙarshe da zan fito takarar”

Atiku ya yi takarar shugaban ƙasar a lokuta da dama.

Ya nemi tsayawa takarar shugaban kasa a shekarar 1993 a karkashin jam’iyyar SDP inda daga baya ya bar wa Moshood Abiola, da kuma Action Congress a shekarar 2007, inda marigayi Umaru Musa Yar’Adua ya lashe zaɓen.

Atiku ya kuma tsaya takara a shekarar 2011 karkashin jam’iyyar ACN, inda ya sha kaye a hannun tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan.

Ya koma jam’iyyar PDP ya tsaya takarar shugaban kasa a zaben 2019, inda ya sha kaye a hannun tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari.

A 2023, ya sake fitowa takarar a PDP amma ya sha kaye a hannun Shugaba Bola Tinubu na APC.

 

 

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Raphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - AtikuCOAS Ya Bukaci Bojojin Nijeriya da su Mayar da Hankali Wajen Kare Rayukan Fararen HulaTURA TA KAI BANGO: Bayan Mutuwar Bashar Sani, Dole ne Arewa Ta Fuskanci MatsalolintaDangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a Edo
X whatsapp