Home SIYASA 2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara – Atiku

2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara – Atiku

Atiku

2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara – Atiku

 

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya Atiku Abubakar, ya ce ba zai sake neman takarar shugaban ƙasar daga 2027 ba.

Ya ce idan aka yi la’akari da shekarunsa da kuma damar da yake da ita ba lallai ya ci gaba da neman damar daga shekara mai zuwa ba.

Atiku ya bayyana hakan ne a wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin na Arise a ranar Laraba.

Da aka tambaye shi game da cikarsa shekaru 80 a shekarar 2027 da yadda hakan zai iya daƙile masa damarsa, Atiku ya ce: “Tabbas za a samu ƙarin masu nema, kuma ita ce dama ta ƙarshe da zan fito takarar”

Atiku ya yi takarar shugaban ƙasar a lokuta da dama.

Ya nemi tsayawa takarar shugaban kasa a shekarar 1993 a karkashin jam’iyyar SDP inda daga baya ya bar wa Moshood Abiola, da kuma Action Congress a shekarar 2007, inda marigayi Umaru Musa Yar’Adua ya lashe zaɓen.

Atiku ya kuma tsaya takara a shekarar 2011 karkashin jam’iyyar ACN, inda ya sha kaye a hannun tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan.

Ya koma jam’iyyar PDP ya tsaya takarar shugaban kasa a zaben 2019, inda ya sha kaye a hannun tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari.

A 2023, ya sake fitowa takarar a PDP amma ya sha kaye a hannun Shugaba Bola Tinubu na APC.

 

 

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp