Home Labarai COAS Ya Bukaci Bojojin Nijeriya da su Mayar da Hankali Wajen Kare...

COAS Ya Bukaci Bojojin Nijeriya da su Mayar da Hankali Wajen Kare Rayukan Fararen Hula

Shugaban Rundunar Sojin Kasa ta Najeriya (COAS), Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya bukaci jami’ai da dakarun sojin kasar su mutunta hakkin bil’adama tare da ba da fifiko ga kare rayukan fararen hula a dukkan ayyukan soja.

Ya bayyana haka ne yayin da yake batar da Makala mai take (Command Philosophy) ga dakarun da suka halarci kwas a Kwalejin koyon dabarun yaki dake birnin tarayya Abuja a ranar Talata

Shaibu ya jaddada cewa bin dokokin ƙasa da ƙasa da suka shafi yaƙi, ciki har da dokokin jin ƙai na duniya (International Humanitarian Law) da kuma ƙa’idojin aiki na soja wato (Rules of Engagement), ba wai kawai wajibi ne a doka kadai ba, har ma yana da muhimmanci wajen samun nasara a fagen daga.

A cewarsa, wannan tsari zai taimaka wa jami’ai su yi aiki yadda ya kamata a cikin yanayin tsaro mai rikitarwa da ke sauyawa a kullum.

Shaibu, ya bayyana cewa sabbin dabarun aikin sojin Najeriya na ci gaba da inganta bisa yadda rundunar ke tinkarar barazanar tsaro na zamani, musamman irin na yaƙin ‘yan tada ƙayar baya, wanda haɗa kai da fararen hula ke da matuƙar muhimmanci wajen samun nasara.

A nasa jawabin, kwamandan Kwalejin koyon dabarun yaki, Manjo Janar Umar Alkali, ya yabawa COAS bisa ci gaba da bai wa makarantar goyon baya, yana mai cewa jawabin ya ƙara wa mahalarta da makarantar ilimi da kwarewa sosai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp