Home Labarai COAS Ya Bukaci Bojojin Nijeriya da su Mayar da Hankali Wajen Kare...

COAS Ya Bukaci Bojojin Nijeriya da su Mayar da Hankali Wajen Kare Rayukan Fararen Hula

Shugaban Rundunar Sojin Kasa ta Najeriya (COAS), Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya bukaci jami’ai da dakarun sojin kasar su mutunta hakkin bil’adama tare da ba da fifiko ga kare rayukan fararen hula a dukkan ayyukan soja.

Ya bayyana haka ne yayin da yake batar da Makala mai take (Command Philosophy) ga dakarun da suka halarci kwas a Kwalejin koyon dabarun yaki dake birnin tarayya Abuja a ranar Talata

Shaibu ya jaddada cewa bin dokokin ƙasa da ƙasa da suka shafi yaƙi, ciki har da dokokin jin ƙai na duniya (International Humanitarian Law) da kuma ƙa’idojin aiki na soja wato (Rules of Engagement), ba wai kawai wajibi ne a doka kadai ba, har ma yana da muhimmanci wajen samun nasara a fagen daga.

A cewarsa, wannan tsari zai taimaka wa jami’ai su yi aiki yadda ya kamata a cikin yanayin tsaro mai rikitarwa da ke sauyawa a kullum.

Shaibu, ya bayyana cewa sabbin dabarun aikin sojin Najeriya na ci gaba da inganta bisa yadda rundunar ke tinkarar barazanar tsaro na zamani, musamman irin na yaƙin ‘yan tada ƙayar baya, wanda haɗa kai da fararen hula ke da matuƙar muhimmanci wajen samun nasara.

A nasa jawabin, kwamandan Kwalejin koyon dabarun yaki, Manjo Janar Umar Alkali, ya yabawa COAS bisa ci gaba da bai wa makarantar goyon baya, yana mai cewa jawabin ya ƙara wa mahalarta da makarantar ilimi da kwarewa sosai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp