Home Labarai COAS Ya Bukaci Bojojin Nijeriya da su Mayar da Hankali Wajen Kare...

COAS Ya Bukaci Bojojin Nijeriya da su Mayar da Hankali Wajen Kare Rayukan Fararen Hula

Shugaban Rundunar Sojin Kasa ta Najeriya (COAS), Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya bukaci jami’ai da dakarun sojin kasar su mutunta hakkin bil’adama tare da ba da fifiko ga kare rayukan fararen hula a dukkan ayyukan soja.

Ya bayyana haka ne yayin da yake batar da Makala mai take (Command Philosophy) ga dakarun da suka halarci kwas a Kwalejin koyon dabarun yaki dake birnin tarayya Abuja a ranar Talata

Shaibu ya jaddada cewa bin dokokin ƙasa da ƙasa da suka shafi yaƙi, ciki har da dokokin jin ƙai na duniya (International Humanitarian Law) da kuma ƙa’idojin aiki na soja wato (Rules of Engagement), ba wai kawai wajibi ne a doka kadai ba, har ma yana da muhimmanci wajen samun nasara a fagen daga.

A cewarsa, wannan tsari zai taimaka wa jami’ai su yi aiki yadda ya kamata a cikin yanayin tsaro mai rikitarwa da ke sauyawa a kullum.

Shaibu, ya bayyana cewa sabbin dabarun aikin sojin Najeriya na ci gaba da inganta bisa yadda rundunar ke tinkarar barazanar tsaro na zamani, musamman irin na yaƙin ‘yan tada ƙayar baya, wanda haɗa kai da fararen hula ke da matuƙar muhimmanci wajen samun nasara.

A nasa jawabin, kwamandan Kwalejin koyon dabarun yaki, Manjo Janar Umar Alkali, ya yabawa COAS bisa ci gaba da bai wa makarantar goyon baya, yana mai cewa jawabin ya ƙara wa mahalarta da makarantar ilimi da kwarewa sosai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
'Yan Daba Sun Farmaki Kasuwar Sayar da Wayoyin Hannu a Jihar KanoFarfesoshi Adamu da Pate: Manyan Gwarzayen Ilimin Sadarwa Masu Taimako Daga Yushau A. ShuaibKotu: Shuaib ya ƙi Buƙatar NIPSS na Shirin Kwace Makullin Ɗakinsa a Shari’ar SEC 47Binciken Gaskiya: Shin Faɗan Oba Femi da Brock Lesnar a Wrestlemania Gaskiya ne ?An Ceto Marayu 15 Daga Hannun ƴan Bindiga a Jihar Kogi'Yan Bindiga sun Kashe Fasto da Iyalansa a Jihar PlateauCikakken Bayani Game da Kitsa Juyin Mulki a NajeriyaIdan Suna Buƙatar Tattaunawa, sa kira mu - Trump ga Iran'Yan Bindiga Sun Kai Hari Dakunan Kwanan Dalibai a Jami'ar OOUAn Kama Mai Taimakawa 'Yan Kungiyar Lakurawa Wajen Samun Kudi a Jihar Sokoto2027: Jam’iyyun Adawa Sun Sanar da Shirinsu na Yakar Tinubu da APC'Yan Siyasa ba sa yi wa Talakawan da Suke Jagoranta Adalci - Sanata NingiRahoton ‘Yan Sanda ya Danganta Kashi 70% na Laifuka a Kano da Shaye-Shayen Miyagun Ƙwayoyi, Ya Gano Mutane 513 da ake Zargin Masu Safara NePantami Ya Samu Karfin Gwiwa Yayin Da Jama'a Ke Taya Shi Murna a Lokacin Ziyarar Ayyuka a GombeMa’aikatar Tsaro ta yi Karin Bayani Kan Yarjejeniyar Yaki da Ta’addanci da Turkiyya, ta Karyata Zargin ‘Jihadi’
X whatsapp