Home SIYASA Jam’iyyar ADC ta Kori Nafi’u Bala Gombe

Jam’iyyar ADC ta Kori Nafi’u Bala Gombe

Nafi'u Bala Gombe

Jam’iyyar ADC ta Kori Nafi’u Bala Gombe

 

Jam’iyyar adawa ta ADC ta kori tsohon maitaimakin jam’iyyar na ƙasa mai iƙirarin shugabancin Jam’iyyar Nafi’u Bala Gombe da wani mamba na jam’iyyar Leke Abejide. Jam’iyyar ta sanar da hakan ne a yayin taronta na ƙasa da ta gudanar.

An kori Nafi’u Gombe ne dalilin “yi wa jam’iyya zagon ƙasa”, kamar yadda Faisal Kabiru ɗaya daga cikin masu magana da jam’iyyar ya shaida wa BBC Hausa, wanda hakan ya jefe jam’iyyar cikin mawuyacin hali.

An kori nafi’u Gombe tare da wasu da suka haɗa da Kenneth Ehiator daga Abia wanda shi ma yake iƙirarin shugabancin jam’iyya a jihar, da Stella Chukwu da kuma Elias Adiukwu.

Nafi’u da ya dage kan zama shugaban jam’iyyar ya fitar da sanarwar waɗanda suka shiga jam’iyyar su Sanata Rabi’u Musa Kwankwanso ba halastattun ‘yan jam’iyya ba ne, saboda sun shiga ba ta hannunsa ba, kazalika katin ‘yan jam’iyyarsu a shi da wani amfani.

Ya kuma jagoranci zanga-zangar da aka yi a Abuja, wadda ta mayar da hankali wajen neman hukumar zaɓe INEC ta yarda da shi a matsayin halastaccen shugaban ADC.

 

`

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Raphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - AtikuCOAS Ya Bukaci Bojojin Nijeriya da su Mayar da Hankali Wajen Kare Rayukan Fararen HulaTURA TA KAI BANGO: Bayan Mutuwar Bashar Sani, Dole ne Arewa Ta Fuskanci MatsalolintaDangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a Edo
X whatsapp