Jam’iyyar ADC ta Kori Nafi’u Bala Gombe
Jam’iyyar adawa ta ADC ta kori tsohon maitaimakin jam’iyyar na ƙasa mai iƙirarin shugabancin Jam’iyyar Nafi’u Bala Gombe da wani mamba na jam’iyyar Leke Abejide. Jam’iyyar ta sanar da hakan ne a yayin taronta na ƙasa da ta gudanar.
An kori Nafi’u Gombe ne dalilin “yi wa jam’iyya zagon ƙasa”, kamar yadda Faisal Kabiru ɗaya daga cikin masu magana da jam’iyyar ya shaida wa BBC Hausa, wanda hakan ya jefe jam’iyyar cikin mawuyacin hali.
Read Also:
An kori nafi’u Gombe tare da wasu da suka haɗa da Kenneth Ehiator daga Abia wanda shi ma yake iƙirarin shugabancin jam’iyya a jihar, da Stella Chukwu da kuma Elias Adiukwu.
Nafi’u da ya dage kan zama shugaban jam’iyyar ya fitar da sanarwar waɗanda suka shiga jam’iyyar su Sanata Rabi’u Musa Kwankwanso ba halastattun ‘yan jam’iyya ba ne, saboda sun shiga ba ta hannunsa ba, kazalika katin ‘yan jam’iyyarsu a shi da wani amfani.
Ya kuma jagoranci zanga-zangar da aka yi a Abuja, wadda ta mayar da hankali wajen neman hukumar zaɓe INEC ta yarda da shi a matsayin halastaccen shugaban ADC.
`











