Home SIYASA Jam’iyyar ADC ta Kori Nafi’u Bala Gombe

Jam’iyyar ADC ta Kori Nafi’u Bala Gombe

Nafi'u Bala Gombe

Jam’iyyar ADC ta Kori Nafi’u Bala Gombe

 

Jam’iyyar adawa ta ADC ta kori tsohon maitaimakin jam’iyyar na ƙasa mai iƙirarin shugabancin Jam’iyyar Nafi’u Bala Gombe da wani mamba na jam’iyyar Leke Abejide. Jam’iyyar ta sanar da hakan ne a yayin taronta na ƙasa da ta gudanar.

An kori Nafi’u Gombe ne dalilin “yi wa jam’iyya zagon ƙasa”, kamar yadda Faisal Kabiru ɗaya daga cikin masu magana da jam’iyyar ya shaida wa BBC Hausa, wanda hakan ya jefe jam’iyyar cikin mawuyacin hali.

An kori nafi’u Gombe tare da wasu da suka haɗa da Kenneth Ehiator daga Abia wanda shi ma yake iƙirarin shugabancin jam’iyya a jihar, da Stella Chukwu da kuma Elias Adiukwu.

Nafi’u da ya dage kan zama shugaban jam’iyyar ya fitar da sanarwar waɗanda suka shiga jam’iyyar su Sanata Rabi’u Musa Kwankwanso ba halastattun ‘yan jam’iyya ba ne, saboda sun shiga ba ta hannunsa ba, kazalika katin ‘yan jam’iyyarsu a shi da wani amfani.

Ya kuma jagoranci zanga-zangar da aka yi a Abuja, wadda ta mayar da hankali wajen neman hukumar zaɓe INEC ta yarda da shi a matsayin halastaccen shugaban ADC.

 

`

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp