Home Taska Jihohin da Zasu fi Fuskantar Matsanancin Yanayin Zafi – NiMet

Jihohin da Zasu fi Fuskantar Matsanancin Yanayin Zafi – NiMet

NiMet

Jihohin da Zasu fi Fuskantar Matsanancin Yanayin Zafi – NiMet

 

Hukumar Kula da Yanayi ta Najeriya (NiMET) ta yi gargaɗin cewa za a samu matsanancin yanayin zafi a ƙasar, inda ta ce hakan zai iya kai wasu ga shiga yanayin galabaita saboda zafin a wasu sassan ƙasar.

A wata sanarwa da ta fitar a shafukanta, NiMet ta ce yanayin zafin zai fi shafar jihohin arewacin ƙasar da suka haɗa da jihohin Neja da Kebbi da Kano da Sokoto da Zamfara da Katsina da Yobe da Jigawa da Bauchi da Gombe da Borno da kuma Adamawa.

A cewar sanarwar, akwai yiwuwar wasu jihohin ma da ba a ambata ba su samu ƙaruwar yanayin na zafi.

A hasashen ta, yanayin zafin zai iya kai wa maki 40 zuwa 45 a ma’aunin salshiyas a arewacin ƙasar, yayin da tsakiyar ƙasar kuma zai kai tsakanin maki 35 zuwa 38 a ma’aunin salshiyas, a Kudancin ƙasar kuma yanayin na iya kai wa maki 33 zuwa 35.

Hukumar yanayin ta buƙaci alumma su riƙa shan ruwa sosai, sannan su kasance a wuri mai iska sosai tare da kaucewa wurare masu cinkoson alumma, kuma su rage zama ƙarƙashin rana.

Ta kuma shawarce su da su sanya hula da gilashi idan za su fita, kuma su sanya kaya marasa nauyi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp