Home Labarai Badaƙalar Kuɗi: Kotu ta Yanke wa Saleh Mamman Shekara 75 a Gidan...

Badaƙalar Kuɗi: Kotu ta Yanke wa Saleh Mamman Shekara 75 a Gidan Yari

Saleh Mamman

Badaƙalar Kuɗi: Kotu ta Yanke wa Saleh Mamman Shekara 75 a Gidan Yari

 

Babbar Kotun Tarayya a Abuja ta yanke wa tsohon ministan lantarki a Najeriya shekara 75 a gidan yari kan almundahanar fiye da naira biliyan 33.

Alƙalin James Omotosho ya yanke hukuncin bayan ya samu Mamman da laifin aikata laifuka 12 da hukumar yaƙi da masu yi wa arzikin ƙasa ta’annati EFCC ta tuhume shi da su masu alaƙa da haɗa baki da almundahana.

EFCC ta tabbatar da hukuncin kotun a saƙon da ta wallafa a shafinta na Fesbuk.

Alƙali Omotosho ya ce ya kamata hukuncin zaman gidan yarin ya soma aiki daga ranar da aka kama mai laifin kasancewar an yanke hukuncin ne ba ya harabar kotun.

Kotun ta kuma umarci hukumomin tsaro da su kamo tsohon ministan a duk inda yake sannan kuma a miƙa wa gwamnati kuɗaɗe da dukiyoyin da aka ƙwato daga hannunsa.

Kotun ta kuma nemi Mamman da ya mayar da naira biliyan 22 na kuɗaɗen aikin samar da cibiyoyin lantarki na Mambila da Zungeru.

An gabatar da Mamman gaban babbar kotun tarayya a Abuja cikin Yulin 2024 bisa tuhume-tuhume 12 da ke da alaƙa da haɗin baki da almundahana. Ya musanta aikata zarge-zargen.

Sai dai a lokacin shari’ar, EFCC ta gabatar da shaidu 17 tare da miƙa wasu bayanai gaban kotun.

Hukuncin da aka yanke a yanzu ya kawo ƙarshen wata babbar shari’ar cin hanci da rashawa da ta fara tun bayan kama tare da tsare Mamman da EFCC ta yi a ranar 10 ga Mayun 2021.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp