Home SIYASA Majalisar Dattawa ta Amince da Nadin Ministoci Biyu

Majalisar Dattawa ta Amince da Nadin Ministoci Biyu

Senate P

Majalisar Dattawa ta Amince da Nadin Ministoci Biyu

Abuja, Nigeria – Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin Ambasada Sola Enikanolaiye a matsayin Karamin Ministan Harkokin Waje.

Haka zalika Majalisar ta amince da nadin Joseph Olasunkanmi Tegbe a matsayin Ministan Wutar Lantarki kamar yadda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bukata.

Majalisa ta amince da nadin ministoci 2

Jaridar Punch ta ruwaito cewa amincewar ta biyo bayan tantancewar da aka yi wa wadanda aka nada a zaman majalisar dattawa, inda aka yi musu tambayoyi kafin yanke hukuncin karshe.

Tun farko, Tinubu, a wasiku daban-daban da ya aika wa majalisar a ranar Talata, ya nemi amincewarta kan nadin sababbin ministocin bisa tanadin kundin tsarin mulki.

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio ne ya karanta wasikun a zauren majalisar, kamar yadda jaridar Vanguard ta ruwaito.

Daga nan aka mika batun ga kwamitin gaba daya domin duba shi cikin gaggawa, kamar yadda dokokin majalisa suka tanada.

Takaitaccen bayani kan ministocin

Tabbatar da nadin Enikanolaiye a matsayin karamin ministan harkokin waje ya tabbatar da dawowarsa sahun gaba a harkokin diflomasiyyar Najeriya.

Dan asalin jihar Kogi, sabon ministan ya taba rike Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban kasa kan harkokin waje da dangantakar kasa da kasa, ya kuma rika babban sakataren ma’aikatar harkokin waje.

A bangaren Tegbe kuwa, nadinsa ya zo a wani lokaci mai muhimmanci ga bangaren lantarki, wanda ke fama da matsalolin karancin kudi da kayan aiki duk da gyare-gyaren da gwamnati ke yi karkashin shirin “Renewed Hope.”

Dalilin nada sabon Ministan Lantarki

Nadinsa ya biyo bayan murabus din tsohon Ministan Wutar Lantarki, Adebayo Adelabu, wanda ya sauka a watan Maris 2026 domin shiga takarar gwamnan jihar Oyo a zaben 2027.

Tegbe, dan asalin jihar Oyo, yana da gogewa fiye da shekaru 30 a fannin manufofin tattalin arziki da gyare-gyare a bangaren gwamnati da masu zaman kansu.

Ya taba zama babban abokin hulda kuma shugaban sashen shawarwari a kamfanin KPMG Africa, kuma a yanzu shi ne Darakta Janar kuma mai kula da hulda tsakanin Najeriya da China.

Haka kuma ya jagoranci kwamitin aiwatar da manufofin haraji na kasa da aka kafa a 2025, tare da taka rawa a gyare-gyaren dokoki da cibiyoyi a bangaren lantarki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp