Home SIYASA Majalisar Dattawa ta Amince da Nadin Ministoci Biyu

Majalisar Dattawa ta Amince da Nadin Ministoci Biyu

Senate P

Majalisar Dattawa ta Amince da Nadin Ministoci Biyu

Abuja, Nigeria – Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin Ambasada Sola Enikanolaiye a matsayin Karamin Ministan Harkokin Waje.

Haka zalika Majalisar ta amince da nadin Joseph Olasunkanmi Tegbe a matsayin Ministan Wutar Lantarki kamar yadda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bukata.

Majalisa ta amince da nadin ministoci 2

Jaridar Punch ta ruwaito cewa amincewar ta biyo bayan tantancewar da aka yi wa wadanda aka nada a zaman majalisar dattawa, inda aka yi musu tambayoyi kafin yanke hukuncin karshe.

Tun farko, Tinubu, a wasiku daban-daban da ya aika wa majalisar a ranar Talata, ya nemi amincewarta kan nadin sababbin ministocin bisa tanadin kundin tsarin mulki.

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio ne ya karanta wasikun a zauren majalisar, kamar yadda jaridar Vanguard ta ruwaito.

Daga nan aka mika batun ga kwamitin gaba daya domin duba shi cikin gaggawa, kamar yadda dokokin majalisa suka tanada.

Takaitaccen bayani kan ministocin

Tabbatar da nadin Enikanolaiye a matsayin karamin ministan harkokin waje ya tabbatar da dawowarsa sahun gaba a harkokin diflomasiyyar Najeriya.

Dan asalin jihar Kogi, sabon ministan ya taba rike Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban kasa kan harkokin waje da dangantakar kasa da kasa, ya kuma rika babban sakataren ma’aikatar harkokin waje.

A bangaren Tegbe kuwa, nadinsa ya zo a wani lokaci mai muhimmanci ga bangaren lantarki, wanda ke fama da matsalolin karancin kudi da kayan aiki duk da gyare-gyaren da gwamnati ke yi karkashin shirin “Renewed Hope.”

Dalilin nada sabon Ministan Lantarki

Nadinsa ya biyo bayan murabus din tsohon Ministan Wutar Lantarki, Adebayo Adelabu, wanda ya sauka a watan Maris 2026 domin shiga takarar gwamnan jihar Oyo a zaben 2027.

Tegbe, dan asalin jihar Oyo, yana da gogewa fiye da shekaru 30 a fannin manufofin tattalin arziki da gyare-gyare a bangaren gwamnati da masu zaman kansu.

Ya taba zama babban abokin hulda kuma shugaban sashen shawarwari a kamfanin KPMG Africa, kuma a yanzu shi ne Darakta Janar kuma mai kula da hulda tsakanin Najeriya da China.

Haka kuma ya jagoranci kwamitin aiwatar da manufofin haraji na kasa da aka kafa a 2025, tare da taka rawa a gyare-gyaren dokoki da cibiyoyi a bangaren lantarki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp