Home SIYASA Majalisar Dattawa ta Amince da Nadin Ministoci Biyu

Majalisar Dattawa ta Amince da Nadin Ministoci Biyu

Senate P

Majalisar Dattawa ta Amince da Nadin Ministoci Biyu

Abuja, Nigeria – Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin Ambasada Sola Enikanolaiye a matsayin Karamin Ministan Harkokin Waje.

Haka zalika Majalisar ta amince da nadin Joseph Olasunkanmi Tegbe a matsayin Ministan Wutar Lantarki kamar yadda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bukata.

Majalisa ta amince da nadin ministoci 2

Jaridar Punch ta ruwaito cewa amincewar ta biyo bayan tantancewar da aka yi wa wadanda aka nada a zaman majalisar dattawa, inda aka yi musu tambayoyi kafin yanke hukuncin karshe.

Tun farko, Tinubu, a wasiku daban-daban da ya aika wa majalisar a ranar Talata, ya nemi amincewarta kan nadin sababbin ministocin bisa tanadin kundin tsarin mulki.

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio ne ya karanta wasikun a zauren majalisar, kamar yadda jaridar Vanguard ta ruwaito.

Daga nan aka mika batun ga kwamitin gaba daya domin duba shi cikin gaggawa, kamar yadda dokokin majalisa suka tanada.

Takaitaccen bayani kan ministocin

Tabbatar da nadin Enikanolaiye a matsayin karamin ministan harkokin waje ya tabbatar da dawowarsa sahun gaba a harkokin diflomasiyyar Najeriya.

Dan asalin jihar Kogi, sabon ministan ya taba rike Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban kasa kan harkokin waje da dangantakar kasa da kasa, ya kuma rika babban sakataren ma’aikatar harkokin waje.

A bangaren Tegbe kuwa, nadinsa ya zo a wani lokaci mai muhimmanci ga bangaren lantarki, wanda ke fama da matsalolin karancin kudi da kayan aiki duk da gyare-gyaren da gwamnati ke yi karkashin shirin “Renewed Hope.”

Dalilin nada sabon Ministan Lantarki

Nadinsa ya biyo bayan murabus din tsohon Ministan Wutar Lantarki, Adebayo Adelabu, wanda ya sauka a watan Maris 2026 domin shiga takarar gwamnan jihar Oyo a zaben 2027.

Tegbe, dan asalin jihar Oyo, yana da gogewa fiye da shekaru 30 a fannin manufofin tattalin arziki da gyare-gyare a bangaren gwamnati da masu zaman kansu.

Ya taba zama babban abokin hulda kuma shugaban sashen shawarwari a kamfanin KPMG Africa, kuma a yanzu shi ne Darakta Janar kuma mai kula da hulda tsakanin Najeriya da China.

Haka kuma ya jagoranci kwamitin aiwatar da manufofin haraji na kasa da aka kafa a 2025, tare da taka rawa a gyare-gyaren dokoki da cibiyoyi a bangaren lantarki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp