Home Labarai An Sauya Farashin Fetur a Matatar Dangote

An Sauya Farashin Fetur a Matatar Dangote

Matatar Dangote

An Sauya Farashin Fetur a Matatar Dangote

 

Jihar Legas – Matatar Man Dangote ta janye ƙarin farashin fetur da ta yi a baya, inda ta mayar da farashin kowace lita na fetur zuwa N1,275.

Sauya farashin na zuwa ne sa’o’i kaɗan bayan sanar da dillalan mai sabon farashi ga ‘yan kasuwa.

Jaridar The Punch ta ce wannan janyewar ta zo ne bayan da matatar man, a farkon ranar Laraba, 6 ga watan Mayun 2026 ta aiwatar da ƙarin farashi zuwa N1,350 kan kowace lita.

An sauya farashin fetur a matatar Dangote

Wani babban jami’i a matatar man Dangote, wanda ya buƙaci a sakaya sunansa, ya tabbatar da ƙarin farashin na farko amma ya ce matatar yanzu ta janye shi.

Ya bayyana cewa an ɗauki wannan shawarar cikin sauri ne sakamakon sauye-sauyen yanayin kasuwa, musamman faɗuwar farashin ɗanyen mai a kasuwannin duniya.

“An janye ƙarin farashin da aka yi a baya. Mun mayar da farashin lita zuwa N1,275,” inji jami’in.

Farashin danyen mai ya sauka Bayanai sun nuna cewa farashin ɗanyen mai ya faɗi ƙasa sosai a safiyar ranar Laraba, inda ɗanyen mai na Brent ya faɗi zuwa dala $101.7 kan kowace ganga.

An yi cinikin danyen mai na West Texas a kan dala $94.11 kan kowace ganga, wanda ke hakan ke nina raguwar kashi 7.48 cikin 100 da kashi 7.98 cikin ɗari bi da bi.

To sai dai, duk da raguwar farashin, binciken da aka gudanar ya nuna cewa gidajen mai da dama sun riga sun ƙara farashin sayarwa ga jama’a zuwa har N1,400 kan kowace lita a Legas.

Matatar Dangote ta ce ba ta yi kari ba

Jaridar The Cable ta kawo rahoton cewa matatar Dangote ta bayyana cewa farashin da take sayar da mai yana nan yadda yake.

A cikin wata sanarwa, matatar Dangote ta bayyana cewa ba ta sauya farashin ba, bayan wasu rahotanni sun nuna cewa an kara shi zuwa N1,350 kan kowace lita.

A cikin watan da ya gabata, Matatar Dangote ta sauya farashin fetur ɗinta sau da dama, sakamakon sauyin kuɗin sayo ɗanyen mai, matsin lamba na farashin canjin kuɗaɗen ƙasashen waje, da kuma yanayin rarraba man a cikin ƙasa.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp