Home Taska Ambaliyar Ruwa a Jigawa: Gidauniyar Ƙasar Qatar da ta Malam Inuwa Sun...

Ambaliyar Ruwa a Jigawa: Gidauniyar Ƙasar Qatar da ta Malam Inuwa Sun Raba Tallafin Abinci ga Mutane 1,000

Tallafi

Ambaliyar Ruwa a Jigawa: Gidauniyar Ƙasar Qatar da ta Malam Inuwa Sun Raba Tallafin Abinci ga Mutane 1,000

 

Biyo bayan iftila’in ambaliyar ruwa da ta afkawa al’ummar Jihar Jigawa a bara, gidauniyar ba da agaji ta Duniya, (Qatar Charity Foundation) da haɗin gwiwar (Gidauniyar Malam Inuwa) ta mai girma shugaban hukumar bunƙasa fasahar sadarwar zamani ta ƙasa, (NITDA), Malam Kashifu Inuwa Abdullahi, (CCIE), sun raba tallafin kayan abinci ga mutane (1,000) daga cikin mutanen da iftila’in ambaliyar ta shafa.

Rabon kayan wanda aka ƙaddamar da shi yau a ofishin gidauniyar da ke kan titin Garun-Gabas, a ƙaramar hukumar Haɗejia, an rabawa mutane (600) nasu waɗanda aka zaƙulo daga ƙananan hukumomi takwas da ke yanƙin ƙasar Haɗejia inda daga bisani za a rabawa sauran yankunan.

Da ya ke bayani jim kaɗan bayan kammala rabon, shugaban gidauniyar Malam Inuwa, Dakta Hussaini Yusuf Baban ya bayyana cewa an warewa yankin ƙasar Haɗejia kason mutum ɗari shida ne duba da girman annobar a yankin.

Da ya ke tsokaci dangane da hanyoyin da su ka bi wajen zaƙulowa gami da tantance mutanen da su ka amfana da tallafin kuwa, Dakta Baban ya bayyana cewa: “Mun tuntuɓi shugabannin ƙananan hukumomi haɗi da Limamai da kuma amintattun mutane wajen haɗa sunayen. Kuma duk wanda mu ka ba wa wannan tallafi ɗaya ne daga cikin mutanen da ruwa ya yi wa ɓarna in ma a gida ko a gona,”. Inji shugaban gidauniyar.

Kayayyakin da aka raba ɗin sun haɗa da: Taliya, Shinkafa, Semovita, wake da Mai. Mutanen da su ka amfanan sun yi godiya haɗi da addu’ar fatan alkhairi ga gidauniyoyin biyu bisa tallafin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp