Home Taska Ambaliyar Ruwa a Jigawa: Gidauniyar Ƙasar Qatar da ta Malam Inuwa Sun...

Ambaliyar Ruwa a Jigawa: Gidauniyar Ƙasar Qatar da ta Malam Inuwa Sun Raba Tallafin Abinci ga Mutane 1,000

Tallafi

Ambaliyar Ruwa a Jigawa: Gidauniyar Ƙasar Qatar da ta Malam Inuwa Sun Raba Tallafin Abinci ga Mutane 1,000

 

Biyo bayan iftila’in ambaliyar ruwa da ta afkawa al’ummar Jihar Jigawa a bara, gidauniyar ba da agaji ta Duniya, (Qatar Charity Foundation) da haɗin gwiwar (Gidauniyar Malam Inuwa) ta mai girma shugaban hukumar bunƙasa fasahar sadarwar zamani ta ƙasa, (NITDA), Malam Kashifu Inuwa Abdullahi, (CCIE), sun raba tallafin kayan abinci ga mutane (1,000) daga cikin mutanen da iftila’in ambaliyar ta shafa.

Rabon kayan wanda aka ƙaddamar da shi yau a ofishin gidauniyar da ke kan titin Garun-Gabas, a ƙaramar hukumar Haɗejia, an rabawa mutane (600) nasu waɗanda aka zaƙulo daga ƙananan hukumomi takwas da ke yanƙin ƙasar Haɗejia inda daga bisani za a rabawa sauran yankunan.

Da ya ke bayani jim kaɗan bayan kammala rabon, shugaban gidauniyar Malam Inuwa, Dakta Hussaini Yusuf Baban ya bayyana cewa an warewa yankin ƙasar Haɗejia kason mutum ɗari shida ne duba da girman annobar a yankin.

Da ya ke tsokaci dangane da hanyoyin da su ka bi wajen zaƙulowa gami da tantance mutanen da su ka amfana da tallafin kuwa, Dakta Baban ya bayyana cewa: “Mun tuntuɓi shugabannin ƙananan hukumomi haɗi da Limamai da kuma amintattun mutane wajen haɗa sunayen. Kuma duk wanda mu ka ba wa wannan tallafi ɗaya ne daga cikin mutanen da ruwa ya yi wa ɓarna in ma a gida ko a gona,”. Inji shugaban gidauniyar.

Kayayyakin da aka raba ɗin sun haɗa da: Taliya, Shinkafa, Semovita, wake da Mai. Mutanen da su ka amfanan sun yi godiya haɗi da addu’ar fatan alkhairi ga gidauniyoyin biyu bisa tallafin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp