Home Taska Rigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka – Hukumar Lafiya...

Rigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka – Hukumar Lafiya ta Duniya

Rigakafi

Rigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka – Hukumar Lafiya ta Duniya

 

Wani rahoto da Hukumar Lafiya ta Duniya ta fitar ya bayyana cewa allurar rigakafin ƙyanda na yara da ake yi ya ceci rayukan kusan mutum miliyan 20 a Afrika cikin shekaru 25 na ƙarnin da ya gabata.

Alkaluman da aka tattara tare da haɗin gwiwar shirin rigakafin GAVI, sun nuna adadin mutuwar da ake samu sakamakon cutar kyanda ya ragu a tsawon wancan lokacin.

Kasashen Cape Verde da Mauritius da Seychelles a bara sun zama kasashe na farko a yankin kudu da hamadar Sahara da suka kawar da cutar gaba daya.

Ci gaban da aka samu ya ƙara bayyana ƙoƙarin da ake yi na faɗaɗa shirye-shiryen rigakafin yara ciki har da na cututtuka kamar ciwon sanƙarau da zazzaɓin cizon sauro.

Amma masana sun yi gargaɗin cewa hallau akwai ƙalubale saboda har yanzu miliyoyin yara ba su samu allurar kariya daga cutar ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp