Home Taska Hukumar NAPTIP ta Ceto Mutane 15 Daga Hannun Masu Safarar Mutane a...

Hukumar NAPTIP ta Ceto Mutane 15 Daga Hannun Masu Safarar Mutane a Jihar Nasarawa

NAPTIP

Hukumar NAPTIP ta Ceto Mutane 15 Daga Hannun Masu Safarar Mutane a Jihar Nasarawa

 

Hukumar yaƙi da safarar mutane a Najeriya NAPTIP ta kuɓutar da mutum 15 har da baƙi bayan da ta bankaɗo wata ƙungiyar masu safarar mutane da ake zargi tana aiki a matsayin kamfanin tallata kayayyaki ta intanet a jihar Nasarawa.

NAPTIP ta kuɓutar da mutanen ne bayan samamen da jami’anta suka kai ƙananan hukumomin Karu da Keffi sakamakon sahihan bayanan da suka samu a kan kamfanin.

NAPTIP ta sanar da haka ne cikin sanarwar da ta wallafa a shafinta na X ranar Laraba.

Ta ce an kai samamen ne a ranar 7 ga watan Mayu inda ta ce cikin mutanen da aka kuɓutar akwai mata huɗu da maza 11. Cikin mazan, uku ƴan Najeriya ne sai sauran da suka fito daga wasu ƙasashen.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp