Hukumar EFCC ta Gurfanar da Ma’aurata Kan Damfarar Kudi Kusan N2bn
Ekiti – Hukumar EFCC ta gurfanar da wani da ke ikirarin shi boka ne, Olorunbukunmi Taiwo, tare da matarsa, Awolegan Omolola Omotola, kan zargin damfarar kudi da suka kusan Naira biliyan biyu.
An gurfanar da ma’auratan ne a gaban Mai shari’a Abubakar Usman na babbar kotun tarayya da ke zamanta a Ado-Ekiti bisa tuhume-tuhume shida.
Yadda EFCC ta kama miji da mata
Rahoton shari’ar da EFCC ta wallafa a shafinta na X ya nuna cewa tuhume tuhumen shida sun shafi damfara da boye kudaden da ake zargin an samu ta haramtacciyar hanya.
EFCC ta sanar da cewa ta kama wadanda ake zargin ne bayan wata mata mai makarantar kudi a jihar Delta, Anazia Colina Kenechukwu, ta shigar da korafi a kansu.
Matar ta bayyana cewa Taiwo ya tuntube ta yana neman ta ba shi kudin da zai yi amfani da su wajen gudanar da wata kwangilar gina hanya da ya ce hukumar DESOPADEC ta ba shi.
A cewarta, ta tura jimillar kudin da suka kai N1,980,000,000 zuwa asusun Taiwo da ke bankin Access Bank.
Read Also:
Sai dai binciken EFCC ya gano cewa an karkatar da kudaden wajen sayen kadarori biyu a Ado-Ekiti.
Kadarorin da EFCC ta kwace
Hukumar ta bayyana cewa ma’auratan sun sayi wani wurin shakatawa mai suna Town Tavern Lounge da wani gida mai dakuna hudu da kudaden da ake zargin an samu ta damfara.
An ce kadarorin suna yankin Ikere Road da Florence Court a Ado-Ekiti.
EFCC ta ce ta samu umarnin kotu a ranar 25 ga Mayu, 2026 domin karbe kadarorin na wucin gadi yayin da ake ci gaba da bincike.
Abin da tuhumar EFCC ta kunsa
Daya daga cikin tuhume-tuhumen ya nuna cewa ma’auratan sun karbi N1,098,961,500 daga hannun matar ta hanyar karya cewa za a yi amfani da kudin wajen gudanar da kwangilar gina hanya.
Ana zarginsu da aikata laifin da ya saba wa dokar damfara ta AFFOFRO ta shekarar 2006, kuma ma’auratan sun musanta aikata dukkan tuhume-tuhumen a lokacin da aka karanta musu a kotu.
Lauyan EFCC, Sesan Ola, ya roki kotu ta sanya ranar fara shari’a tare da bayar da umarnin tsare wadanda ake zargin.
Mai shari’a Abubakar Usman ya dage sauraron karar zuwa ranar Alhamis, 11 ga Yunin 2026, kuma ya bayar da umarnin a ci gaba da tsare ma’auratan a hannun EFCC har zuwa ranar da za a sake zama.










