Home Taska Gwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026

Gwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026

Gwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026

 

Gwamnatin Najeriya ta ƙudiri anyiar samun naira tiriliyan 2.5 na kuɗaɗen shiga na cikin gida a shekarar 2026.

Mukaddashin Shugaban Hukumar Kula da Ɗa’a a Harkokin Kasafin Kuɗi ta Ƙasa, Charles Abana ne ya bayyana hakan yayin wata ganawa tsakanin shugabannin hukumar da Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume, a Abuja.

A wata sanarwa da mai magana da yawun Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya, Chris Ugwuegbulam, ya fitar, Mista Abana ya ce an ɗauki wannan mataki ne bayan hukumar ta sa ido kan kuɗaɗen shiga na kusan naira tiriliyan 1.84 da ma’aikatun gwamnati da hukumominta suka samar zuwa watan Satumban 2025.

Ya ce, “Ta hanyar ƙara sa ido kan rarar kuɗaɗen shiga na kamfanonin gwamnati da kuma kuɗaɗen shiga da ma’aikatu da hukumomin gwamnati ke samarwa, hukumar ta lura da kuɗaɗen shiga na kusan naira tiriliyan 1.84 zuwa watan Satumban 2025, kuma yanzu ta ƙudiri aniyar samun naira tiriliyan 2.5 a matsayin kuɗaɗen shiga na shekarar 2026.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Jami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya 
X whatsapp