Home Taska ‘Yan Sintiri Sun yi Ram da Masu Garkuwa 10 a Dajin Kwara

‘Yan Sintiri Sun yi Ram da Masu Garkuwa 10 a Dajin Kwara

‘Yan Sintiri Sun yi Ram da Masu Garkuwa 10 a Dajin Kwara

‘Yan sintiri a jihar Kwara sun yi ram da wasu mutum goma wadanda ake zarginsu da addabar yankunan Obbo-Aiyegunle zuwa Ekiti.

Kamar yadda kwamandan hukumar sintiri, Alhaji Saka Ibrahim ya sanar, an kama su ne a daji yayin da jami’ai suka kai samame.

Ya sanar da cewa har yanzu mutanensu suna cikin daji kuma za su mika wadanda aka kama ga jami’an ‘yan sanda.

Kwara – Wasu mutum goma da ake zargin masu garkuwa da mutane ne da suka addabi yankin Obbo-Aiyegunle zuwa Ekiti a jihar Kwara sun shiga hannun hukuma.

An damke su ne bayan samamen da jami’ai suka kai wata maboyarsu da ke daji inda ake zargin suna adana wadanda suka sace, Daily Trust ta ruwaito hakan.

Yankin a cikin kwanakin nan ya shahara ta yadda masu garkuwa da mutane ke sace mutane kuma a kan samu gawawwakinsu bayan an biya kudin fansa.

Kwamandan hukumar sintiri ta jihar Kwara, Alhaji Saka Ibrahim, ya tabbatar da aukuwar lamarin ta wata tattaunawar waya da Daily Trust.

Kamar yadda yace:

“An damke wasu mutum bakwai a ranar Talata yayin da aka cafke wasu uku a ranar Laraba. Amma har yanzu jami’anmu na duba dajin. Za mu mika su hannun ‘yan sanda idan sun fito daga dajin.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp