Home Taska Abubuwa 5 da Kuke Bukata Kafin Shiga Aikin Soja a Najeriya

Abubuwa 5 da Kuke Bukata Kafin Shiga Aikin Soja a Najeriya

Abubuwa 5 da Kuke Bukata Kafin Shiga Aikin Soja a Najeriya

 

Rundunar sojojin Najeriya ta fitar da sanarwar daukar sabbin ma’aikata na shekarar 2022/2023.

An nemi wadanda ke da sha’awar shiga aikin soja su ziyarci shafin rundunar na yanar gizo don cike fom.

A nan, mun tattaro wasu abubuwa biyar da dole sai me neman aikin ya cike su

A ranar Talata, 8 ga watan Maris ne, rundunar sojojin Najeriya ta sanar da cewar shirinta na daukar ma’aikata na 2022/2023 na gudana a yanzu haka.

An bukaci wadanda ke sha’awar aikin da su ziyarci shafin daukar aiki na rundunar sojin domin ganin yadda za su nemi aikin, Daily trust ta rahoto.

Idan kana son shiga aiki soja, dole ka cike wadannan abubuwan bukata:

1. Dole ka kasance dan Najeriya sannan ka mallaki katin shaida na dan kasa.

2. Dole ka mallaki akalla kredit 5, ciki harda Ingilishi a jarrabawar WASSCE, GCE, NECO ko NAPTIB a zama da bai wuci biyu ba.

3. Dole mutum ya kasance da lafiyar jiki da na kwakwalwa kuma kada mutum ya yi kasa da mita 1.68 ga maza ko kuma 1.62 ga mata.

4. Dole mutum ya kasance tsakanin shekara 18 da 26.

5. Dole ne a cire fom din da aka cike ta yanar gizo, a sanya hannu akai sannan a zo dashi cibiyar jarrabawa yayin da aka fara tantance wadanda za su shiga aikin

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

Comments are closed.

Latest News
COAS Ya Bukaci Bojojin Nijeriya da su Mayar da Hankali Wajen Kare Rayukan Fararen HulaTURA TA KAI BANGO: Bayan Mutuwar Bashar Sani, Dole ne Arewa Ta Fuskanci MatsalolintaDangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige Fubara
X whatsapp