Home Taska Abubuwa 5 da Kuke Bukata Kafin Shiga Aikin Soja a Najeriya

Abubuwa 5 da Kuke Bukata Kafin Shiga Aikin Soja a Najeriya

Abubuwa 5 da Kuke Bukata Kafin Shiga Aikin Soja a Najeriya

 

Rundunar sojojin Najeriya ta fitar da sanarwar daukar sabbin ma’aikata na shekarar 2022/2023.

An nemi wadanda ke da sha’awar shiga aikin soja su ziyarci shafin rundunar na yanar gizo don cike fom.

A nan, mun tattaro wasu abubuwa biyar da dole sai me neman aikin ya cike su

A ranar Talata, 8 ga watan Maris ne, rundunar sojojin Najeriya ta sanar da cewar shirinta na daukar ma’aikata na 2022/2023 na gudana a yanzu haka.

An bukaci wadanda ke sha’awar aikin da su ziyarci shafin daukar aiki na rundunar sojin domin ganin yadda za su nemi aikin, Daily trust ta rahoto.

Idan kana son shiga aiki soja, dole ka cike wadannan abubuwan bukata:

1. Dole ka kasance dan Najeriya sannan ka mallaki katin shaida na dan kasa.

2. Dole ka mallaki akalla kredit 5, ciki harda Ingilishi a jarrabawar WASSCE, GCE, NECO ko NAPTIB a zama da bai wuci biyu ba.

3. Dole mutum ya kasance da lafiyar jiki da na kwakwalwa kuma kada mutum ya yi kasa da mita 1.68 ga maza ko kuma 1.62 ga mata.

4. Dole mutum ya kasance tsakanin shekara 18 da 26.

5. Dole ne a cire fom din da aka cike ta yanar gizo, a sanya hannu akai sannan a zo dashi cibiyar jarrabawa yayin da aka fara tantance wadanda za su shiga aikin

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

Comments are closed.

Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp