Home WASANNI Kocin Najeriya Augustine Eguavoen na Fatan Dawo da Victor Moses

Kocin Najeriya Augustine Eguavoen na Fatan Dawo da Victor Moses

Kocin Najeriya Augustine Eguavoen na Fatan Dawo da Victor Moses

Mai horas da tawagar Super Eagles Augustine Eguavoen na son janyo hankalin tsohon dan wasan Chelsea Victor Moses ya koma bugawa kasarsa da za ta halarci Qatar 2022.

Dan wasan mai shekara 31 da ke taka leda a kungiyar Spartak Moscow da ke Rasha, ya ajiye takalmansa ne a 2018.

Shugaban Hukumar Kwallom Kafa ta Najeriya (NFF) Amaju Pinnick da tsohon kocin Najeriya Gernot Rohr duka sun yi kokarin dawo da dan wasan amma hakarsu ba ta cimma ruwa ba.

Sai dai Eguavoen, wanda ya gaji Rohr a watan Disamba ya ce: “muna son kasarmu ta yi abin arziki.

“Ina son kwallon Victor Moses kuma ina ta kokarin dawo da shi ya ci gaba da bugawa kasarmu.

“Baya cikin tawagarmu da za ta kara da Ghana domin neman gurbi a gasar cin kofin duniya, amma muna sa ran ganinsa a gaba saboda muna son kasar ta yi abin arziki.

“Ko kana so ko baka so yana da gudunmuwar da zai iya bayarwa. Amma a yanzu yana wasa a Rasha, kuma mun san duk matsalar da take faruwa tsakanin Rasha da Ukrain. Cikin farin ina sanar da cewa tattaunawarmu da shi ta fara nisa.”

Moses ya koma Spartak daga Chelsea a 2021, sai dai zai iya sauya kungiya a makonni masu zuwa

Fifa ta shaida wa duk wasu ‘yan wasa da ke taka leda a Rasha su dakatar da kwataraginsu da kasar su kuma fice cikin kankanin lokaci.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp