Home WASANNI Kocin Najeriya Augustine Eguavoen na Fatan Dawo da Victor Moses

Kocin Najeriya Augustine Eguavoen na Fatan Dawo da Victor Moses

Kocin Najeriya Augustine Eguavoen na Fatan Dawo da Victor Moses

Mai horas da tawagar Super Eagles Augustine Eguavoen na son janyo hankalin tsohon dan wasan Chelsea Victor Moses ya koma bugawa kasarsa da za ta halarci Qatar 2022.

Dan wasan mai shekara 31 da ke taka leda a kungiyar Spartak Moscow da ke Rasha, ya ajiye takalmansa ne a 2018.

Shugaban Hukumar Kwallom Kafa ta Najeriya (NFF) Amaju Pinnick da tsohon kocin Najeriya Gernot Rohr duka sun yi kokarin dawo da dan wasan amma hakarsu ba ta cimma ruwa ba.

Sai dai Eguavoen, wanda ya gaji Rohr a watan Disamba ya ce: “muna son kasarmu ta yi abin arziki.

“Ina son kwallon Victor Moses kuma ina ta kokarin dawo da shi ya ci gaba da bugawa kasarmu.

“Baya cikin tawagarmu da za ta kara da Ghana domin neman gurbi a gasar cin kofin duniya, amma muna sa ran ganinsa a gaba saboda muna son kasar ta yi abin arziki.

“Ko kana so ko baka so yana da gudunmuwar da zai iya bayarwa. Amma a yanzu yana wasa a Rasha, kuma mun san duk matsalar da take faruwa tsakanin Rasha da Ukrain. Cikin farin ina sanar da cewa tattaunawarmu da shi ta fara nisa.”

Moses ya koma Spartak daga Chelsea a 2021, sai dai zai iya sauya kungiya a makonni masu zuwa

Fifa ta shaida wa duk wasu ‘yan wasa da ke taka leda a Rasha su dakatar da kwataraginsu da kasar su kuma fice cikin kankanin lokaci.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp