Home Labarai ITU Ta nada Pantami Matsayin Jagora a Taron ta na Duniya a...

ITU Ta nada Pantami Matsayin Jagora a Taron ta na Duniya a kasar Switzerland

Kungiyar Sadarwa ta Kasa da Kasa wato International Telecommunication Union (ITU) ta nada Ministan Sadarwa da Tattalin Arziki na Zamani Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami, a matsayin shugaban taron kolin kingiyar da gudana a shalkwatar kungiyar dake Geneva a kasar Switzerland.

Kungiyar Ta ITU ta tabbatar da nadin na Pantami ta cikin wata wasika mai dauke da sa hannun babban sakatern ta, wanda ya bayyana cewa kungiyar ta nada Farfesa Pantami matsayin shugaban taron kolin ta.

”Bisa la’akari da sadaukarwarsa ga kungiya, da kuma rawar da yake takawa a cikin tsare tsaren gudanar da taron na WSIS” masu ruwa da tsaki sunga dacewar nadashi bisa wannan matsayi, taron zai sami halartar manyan ministoci daga kasashen dake cikin wannan kungiya.

Dandalin taron na WSIS 2022 na matsayin babban dandalin tattaunawa gami da rawar da hanyoyin sadarwa ke takawa, kuma tana matsayin hanyar aiwatar da manufofin cigaba mai dorewa, bisa la’akari da tsarin da duniya ke kai gami da bibiyar hanyoyin aiwatar da kudirin cigaba mai dorewa zuwa shekarar 2030 na (UNGA Resolution A/&70/1).

Haka zalika dandamalin na WSIS na bin diddigin nasarorin da ake samu bisa hadin Gwiwar hukumomin Majalisar Dinkin Duniya da abin ya shafa, ta hanayar samar da bayanan binciken da suka gudanar.

Taron na WSIS, na kungiyar ITU da asusun tallafawa kananan yar ana majalisar dinkin duniyar da UNCTAD suka shirya tare da hadin wasu hukumomin majalisar dinkin duniyar guda 24, da suka hadar da FAO, ILO, ITC, UNDESA, UNICO, UNITAR, UNHCR, UNODC, UNEP, UPU, UN TECH BANK, WMO, WIPO, WHO, WFP da dai sauransu.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp