Home General Bikin Kirsimeti da Sabuwar Shekara: FRSC zata girke jami’ai sama da  Dubu ...

Bikin Kirsimeti da Sabuwar Shekara: FRSC zata girke jami’ai sama da  Dubu  36 a Sassa Nijeriya

Bikin Kirsimati da Sabuwar Shekara: FRSC zata girke jami’ai sama da  Dubu  36 a Sassa Nijeriya

Hukumar kiyaye hadurra a Najeriya FRSC, ta sanar da aike jami’anta a sassa daban-daban na kasar domin gudanar da sintiri a tituna yayin gudanar da bukukuwan Kirismeti da na sabuwar shekara da ke tafe.

Wannan na cikin jawabin da mukaddashin shugaban hukumar , Dauda Biu ya yi a yayin da yake ganawa da manema labarai a ranar Litinin, ya ce sun tanadi  jami’ai 36,224 da za su yi wannan aikin.

Sai dai ya ce hukumar na bai wa ‘yan Najeriya tabbacin kare lafiyarsu da dukiya a lokacin da ake gudanar da bukukuwan na  karshen shekarar 2022 lafiya da fatan ganin 2023 da ke tafe.

A Najeriya dai ana yawan samun hadurran motoci a manya da kananan titunan kasar, musamman lokacin bukukuwan karshen shekara.

Hukumar kiyaye hadurra ta kasar da ‘yan sanda na dora alhakin hadurran ababen hawan kan tukin ganganci, ko gudu fiye da kima da direbobi ke yi, sai kuma rashin hakurin masu ababen hawa a lokacin da aka samu cunkoun ababen hawa.

PRNigeria hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
COAS Ya Bukaci Bojojin Nijeriya da su Mayar da Hankali Wajen Kare Rayukan Fararen HulaTURA TA KAI BANGO: Bayan Mutuwar Bashar Sani, Dole ne Arewa Ta Fuskanci MatsalolintaDangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige Fubara
X whatsapp