Dakarun sojojin Nijeriya sun Murkushe ‘Yan Ta’adda a Mafa ta Jihar Borno

Dakarun sojin Nijeriya karkashin rundunar Operation Hadin Kai (OPHK) a Arewa Maso Gabas sun sami Nasarar tarwatsa gungun ‘Yan Boko Haram a wani kwanton Bauna da suka yi musu a kauyen
Troops of Operation kauyen Ngowom dake karamar Hukumar Mafa ta jihar Borno.
Gungun ‘yan ta’addan da aka hallaka Su 20 dake saman babura sun fito daga
Yammacin jihar ta mashiga Mafa akan hanyar su ta zuwa dajin Sambisa.
Zagazola ya ruwaito cewa dakarun sojin sun sami nasarar ne bayan samun wani rahoton sirri kan cewa ‘yan Ta’addan na kan hanyar Mafa
Sojojin bisa hadin Gwiwar dakarun sa kai na JTF suka yi musu kwanton bauna, nan take suka hallaka da dama cikin su.

Haka kuma sun sami nasarar kama guda cikin ‘yan Ta’addan a raye, yayin da wasu suka gudu cikin daji da raunin harbi a jikin su.
“kwanton baunar ya haifar da mummunar musayar wuta tsakanin mu, daga bisani sun fara shirin ranta a na kare, na muka bisu, saboda haka mun halaka da dama daga cikin su, wasu kuwa sun tsere da raunikan harbi a jikin su. A cewa majiyar.
Ya bayyana cewa 2 cikin dakarun CJTF sun ji rauni sakamakon musayar wuta, inda kuma suka sami nasarar kwato makamai da babura a hannun ‘yan Ta’addan

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 15 minutes 13 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 56 minutes 38 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com