Buhari: Zan nesanta kai na da Birnin Abuja bayan 2023

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya sha alwashin nesanta kan sa daga birnin Abuja bayan 29 ga watan Mayu na shekarar 2023, domin kaucewa shugaban da zai gaje shi katsalandan
Shugaban ya bayyana hakan ne lokaci da ya karbi bakuncin mazauna birnin bisa jagorancin ministan birnin Muhammad Bello a fadar shugaban kasa a ranar Lahadi.
A yayin ziyarar gaisuwar bukuwan kirsimeti, shugaban yace zai koma mahaifarsa ta Daura a jihar Katsina da ke Arewacin Najeriya bayan kammala wa’adin shugabancin sa.
Acewar sa kauracewa birnin Abuja shi ne domin bai wa sabon shugaba damar gudanar da aiyukansa ba tare da katsalandan ba.
Haka kuma ya kara da cewa bai gina sabon gida a Daura ko a wani wuri ba, kuma zai koma gidansa domin cigaba da rayuwa bayan cikar wa’adin mulkinsa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 12 minutes 14 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 53 minutes 39 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com