Home Labarai Abba Gida-Gida ya nada Baffa Bichi Matsayin Shugaban Kwamitin Karbar Mulki

Abba Gida-Gida ya nada Baffa Bichi Matsayin Shugaban Kwamitin Karbar Mulki

Zababben gwamnan jihar kano Abba Kabir Yusuf ya nada tsohon shugaban hukumar lura da jami’oin Nijeriya (Tetfund) Dr. Baffa bichi matsayin shugaban kwamitin karbar Mulki.

Wannan na kunshe ne cikin watan sanarwa da sakataren yada labaran zababben Gwamnan Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar wadda aka raba ga manema labarai a yammacin juma’a.

Inda Sanarwar ta bayyana cewa biyo bayan tabbatar masa da shaidar kasancewar s ana zababben gwamnan jihar kano Abba Kabir yusuf ya nada kwamitin karbar Mulki daga hannun gwamanti mai shudewa.

Inda tsohon sakataren hukumar ta tetfund kuma wanda ya yiwa jam’iyyar NNPP takarar sanata a santoriyar kano ta arewa a zaben 2023, Dr. Baffa Bichi matsayin shugaban kwamitin karbar mulkin Abdullahi Musa matsayi sakatare.

Aikin Kwamitin shine gudanar da ayyukan mika mulki cikin tsari daga gwamnatin Ganduje mai barin gado zuwa gwamnatin Abba Gida Gida mai jiran gado.

Mai girma Gwamnan Jihar Kano mai jiran gado zai kaddamar da kwamitin a ranar Asabar 1 ga Afrilu, 2023 da karfe 2:00 na rana. Haka kuma akwai cikakken jerin membobin Babban Kwamiti, yayin da za a sanar da ƙananan kwamitoci a sassa daban-daban.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp