Home Labarai Rundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile...

Rundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindiga

Rundunar sojin ƙasa ta Najeriya ta sanar da tura dakaru na musamman zuwa jihar Filato domin daƙile ayyukan ’yan bindiga da kuma fuskantar sabon ɓarkewar hare-haren rashin tsaro a jihar.

Matakin ya biyo bayan amincewar da Babban hafsan sojin ƙasa, Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya bayar na tura Rundunar ta musamman zuwa yankin.

Sanarwar da rundunar ta fitar ta ce, “dakarun, waɗanda tuni suka isa Jihar Filato, za su gudanar da ayyuka masu tsauri da farmaki kai tsaye domin murkushe ’yan bindiga da sauran masu aikata laifuka.”

Rahotanni sun nuna cewa rundunar na da horo na musamman da kayan aiki na zamani da ake sa ran za su taimaka wajen sauya yanayin tsaro a jihar.

Yayin karɓar dakarun a hedikwatar Rundunar Soji ta 3 Division, babban kwamandan rundunar, Manjo Janar Folusho Oyinlola ya yaba da jagorancin gaggawa da Shugaban Sojin Kasa ya nuna wajen samar da muhimman kayan yaƙi da sauran kayayyakin aiki da za su ba dakarun damar aiwatar da aikinsu yadda ya kamata.

Ya bayyana cewa wannan goyon baya zai taimaka matuƙa wajen cimma nasarar ayyukan tsaro a jihar.

Haka kuma, ya yi kira ga al’ummar Jihar Filato da kada su firgita idan suka ga yawan motsin sojoji da manyan kayan aikin soja.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp