Home Labarai Amurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da...

Amurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci

Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana cewa zai iya sake ƙaddamar da hare-hare a Najeriya matuƙar bai gamsu da ƙoƙarin ƙasar ba wajen daƙile hare-hare a kan kiristoci.

Trump ya bayyana haka ne a ranar Alhamis a lokaci da yake jawabi a ranar addu’a ta ƙasar Amurka karo na 74, wadda aka yi a birnin Washington.

“Duk wanda ya kai wa kiristoci hari, ya san dole Trump zai mayar da martani mai zafi. Na san maganar babu daɗi, amma ita ce magaar gaskiya,” in ji shi.

A lokacin taron addu’ar, Trump ya bayyana zuwan uwargidan Shugaban Najeriya, Remi Tinubu a addu’ar, inda ya yaba mata, sannan ya ce mata ce mai mutunci da ƙima.

Trump na bayani ne kan zargin da ake yi cewa ana yi wa kiristoci kisan kiyashi a Najeriya, lamarin da Amurka ta sa baki, har ta ƙaddamar da hare-hare a ƙasar a bara.

Sai dai Najeriya ta sha nanata cewa kashe-kashen da ake yi a ƙasar ba su da alaƙa da bambancin addini ko ƙabilanci, sannan ta ƙara da cewa tana ƙoƙarinta na magance matsalar.

Trump ya ce hare-haren da ya kai a Najeriya, ya yi ne tare da haɗin gwiwar hukumomin Najeriya, inda ya ce ya amince a kai harin ne domin fatattakar mayaƙan IS.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp