Home Labarai Amurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da...

Amurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci

Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana cewa zai iya sake ƙaddamar da hare-hare a Najeriya matuƙar bai gamsu da ƙoƙarin ƙasar ba wajen daƙile hare-hare a kan kiristoci.

Trump ya bayyana haka ne a ranar Alhamis a lokaci da yake jawabi a ranar addu’a ta ƙasar Amurka karo na 74, wadda aka yi a birnin Washington.

“Duk wanda ya kai wa kiristoci hari, ya san dole Trump zai mayar da martani mai zafi. Na san maganar babu daɗi, amma ita ce magaar gaskiya,” in ji shi.

A lokacin taron addu’ar, Trump ya bayyana zuwan uwargidan Shugaban Najeriya, Remi Tinubu a addu’ar, inda ya yaba mata, sannan ya ce mata ce mai mutunci da ƙima.

Trump na bayani ne kan zargin da ake yi cewa ana yi wa kiristoci kisan kiyashi a Najeriya, lamarin da Amurka ta sa baki, har ta ƙaddamar da hare-hare a ƙasar a bara.

Sai dai Najeriya ta sha nanata cewa kashe-kashen da ake yi a ƙasar ba su da alaƙa da bambancin addini ko ƙabilanci, sannan ta ƙara da cewa tana ƙoƙarinta na magance matsalar.

Trump ya ce hare-haren da ya kai a Najeriya, ya yi ne tare da haɗin gwiwar hukumomin Najeriya, inda ya ce ya amince a kai harin ne domin fatattakar mayaƙan IS.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp