Home Labarai Tinubu ya tura bataliyar soji jihar Kwara

Tinubu ya tura bataliyar soji jihar Kwara

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya bayar da umarnin tura bataliyar soji zuwa sassan jihar Kwara, bayan mummunan harin da ya yi sanadiyyar kisan gomman mutane a ƙaramar hukumar Kaiama ta jihar.

Shugaba Tinubu a wata sanarwa da kakakinsa Bayo Onanuga ya fitar ranar Laraba da dare ya kuma naɗa kwamandan da zai jagoranci rundunar sojin da za a tura jihar Kwara, wadda za ta gudanar da aikin wanzar da zaman lafiya da aka yi wa laƙabi da ‘Operation Savanna Shield’.

Gwamnatin Najeriya ta ɗauki wannan mataki ne bayan harin da aka kai wa ƙauyen Woro, inda rahotanni ke cewa an tattara gawarwakin mutane 78 da maharan suka kashe.

 a wata ganawa da kafar yada labarai ta BBCHausa ta yi da Hon Sa’idu Baba Ahmed, ɗan majalisar dokokin jihar Kwara, ya shaidawa cewa sun yi jana’izar sama da mutane 70 daga cikin waɗanda maharan suka kashe.

Ya ce ”abin da dai na gani, waɗanda muka yi wa sallah, mutum 78 ne amma akwai waɗanda aka ƙone a cikin gidajensu, ba mu san adadin su ba tukun. An hallaka mutum zai kai 170.”

Hon. Baba Ahmed ya kuma ce maharan ”sun wuce da mata 38,” daga ƙauyukan da suka kai wa hari.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp