Home Labarai Gwamnatin Kogi ta ba da umarnin rufe makarantun firamare da na sakandare...

Gwamnatin Kogi ta ba da umarnin rufe makarantun firamare da na sakandare a jihar

Gwamnatin jihar Kogi ta bayar da umarnin rufe makarantun firamare da na sakandare a faɗin jihar, wani mataki da ta ce ta ɗauka don kare lafiyar ɗalibai da kuma malamansu.

Wata sanarwa da kwamishinan yaɗa labarai na jihar Kingsley Fanwo ya fitar, ya ce an ɗauki matakin ne saboda wasu bayanan sirri na tsaro da suka samu, inda suka ga ya dace a ɗauki matakan kare makarantun.

Fanwo ya ce ba a rufe makarantun ba don tayar da hankalin ɗalibai, amma saboda kare lafiyarsu ba wai sai wani abu ya faru ba.

Ya ƙara da cewa gwamna Usman Ododo ya umarci dukkan hukumomi da abin ya shafa da su ɗauki matakai na tabbatar da cewa an koma karatu da zarar an ga babu wani haɗari.

Kwamishinan ya yaba wa jami’an tsaro kan bayar da bayanan sirri a kan lokaci, inda ya kwatanta cewa hakan zai taimaka wa tsarin tsaron jihar.

Ya tabbatar wa mazauna jihar cewa gwamnati na iyaƙar koƙarinta wajen shawo kan lamarin, inda ya ce jami’an tsaro na aiki tukuru don gano da kuma kaƙƙaɓe maɓoyar ɓata-gari a faɗin jihar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp