Home Labarai Gwamnatin Kogi ta ba da umarnin rufe makarantun firamare da na sakandare...

Gwamnatin Kogi ta ba da umarnin rufe makarantun firamare da na sakandare a jihar

Gwamnatin jihar Kogi ta bayar da umarnin rufe makarantun firamare da na sakandare a faɗin jihar, wani mataki da ta ce ta ɗauka don kare lafiyar ɗalibai da kuma malamansu.

Wata sanarwa da kwamishinan yaɗa labarai na jihar Kingsley Fanwo ya fitar, ya ce an ɗauki matakin ne saboda wasu bayanan sirri na tsaro da suka samu, inda suka ga ya dace a ɗauki matakan kare makarantun.

Fanwo ya ce ba a rufe makarantun ba don tayar da hankalin ɗalibai, amma saboda kare lafiyarsu ba wai sai wani abu ya faru ba.

Ya ƙara da cewa gwamna Usman Ododo ya umarci dukkan hukumomi da abin ya shafa da su ɗauki matakai na tabbatar da cewa an koma karatu da zarar an ga babu wani haɗari.

Kwamishinan ya yaba wa jami’an tsaro kan bayar da bayanan sirri a kan lokaci, inda ya kwatanta cewa hakan zai taimaka wa tsarin tsaron jihar.

Ya tabbatar wa mazauna jihar cewa gwamnati na iyaƙar koƙarinta wajen shawo kan lamarin, inda ya ce jami’an tsaro na aiki tukuru don gano da kuma kaƙƙaɓe maɓoyar ɓata-gari a faɗin jihar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp