Home Labarai NNPCL zai dauko ƙwararru daga chaina domin inganta Matatun kasar

NNPCL zai dauko ƙwararru daga chaina domin inganta Matatun kasar

NNPCL

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL ya ce yana tattaunawa da wata matatar man fetur a ƙasar China domin inganta matatun man fetur na Najeriya.

Babban jami’in gudanarwa na kamfanin, Bayo Ojulari ne ya bayyana haka a ranar Laraba, inda ya ce suna buƙatar ƙwararru ne domin mayar da matatun gwamnatin ƙasar su koma aiki da kyau bayan shekarun da suka ɗauka ba sa aiki yadda ya kamata.

Ojulari ya ce nazarin da suka gudanar bayan ya fara aiki ne suka gano cewa ana asarar kuɗi ne maimakon cin riba wajen gudanar da matatun.

Ya ce sun amince da ɗauko ƙwararru waɗanda suka san aikin ɓangaren, maimakon ɗauko ƴan kwangila.

“Shirye-shirye sun yi nisa. Muna ci gaba da tattaunawa da wasu ƙwararru da muke so su inganta mana ayyukan matatun. Kuma gobe wasu daga ciki za su fara zuwa matatun.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp