Rundunar ‘Yan Sanda jihar kano ta fara binkice kan bata garin da suka raunata Musa khan

Kwamishinan ƴan sandan jahar Kano ya aike da tawagar dubiya ga Ɗan jaridar da wasu bata gari suka raunata a eaten Asabar a jihar kano.
Musa Sani Aliyu (Khan) da yake aiki da gidan Radiyo Jalla Fm Kano da Jaridar Arewa Agenda, ya gamu da Aftila’in ne akan hanyarsa ta komawa gida Daga wajen aiki.
Tawagar da kwamishinan ƴan sandan jahar Kanon ya aike ƙarƙashin jagorancin kakakin rundunar ƴan sandan jahar Kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa , ta ziyarci gidan su Musa dake Unguwar Hausawar Mazare dake yankin gidan Zoo Kano.
Kakakin ƴan sandan ya jajantawa ƴan uwan Ɗan jaridar da sauran abokan aiki bisa wannan abu da ya faru.
SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya ƙara da cewa rundunar ta duƙufa wajen gudanar da bincike domin cafko waɗanda ake zargi da aikata wannan lamarin dan su fuskanci hukunci.
PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 15 hours 1 minute 20 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 16 hours 42 minutes 45 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com